Monday, May 25, 2015

Taya Murna Ga Sabon Daktan Sunnah


TAYA MURNA GA SABON DAKTAN SUNNAH

Alhamdulillah, ina amfani da wannan dama nayi Allah godiya da ya kara sanyawa wannan tafiya Sunnah albarka. A jiya Lahadi dan uwa Malam Jamilu Yusufu Zarewa ya samu matsayin Dakta a katafariyar Jami'ar Musulunci ta Madina. Ba shakka muna alfahari da wannan cigaba musamman a fa gen Fiqihu da al'umma ke kishirwarsa. 

Ina maka fatan alheri dan uwa Dr. Jamilu Zarewa, Allah ya yi maka jagoranci yayi riko da hannunka ya yalwata kirjinka. Ina taya ka murna kai da iyalanka na samun wannan daukaka. Allah ya cigaba da amfanar da al'umma da rayuwarka. Alf Alf Mabrouk.

Yasir Ramadan Gwale
26-05-2015

No comments:

Post a Comment