Wednesday, May 27, 2015

Ba zamu Manta Da Zagin Da Akaiwa Manzon Allah SAW A Kano Ba



BA ZAMU MANTA DA ZAGIN DA AKAIWA MANZON ALLAH A KANO BA

Yau a kano, da wani Malamin Izala ne yace "Sai Ya tattaka Wuyan Inyass" da yanzu Kano tana nan kamar za ai tashin alkiyama, su Sheikh Google su yita kurari da barazanar karya, suna kiran Bala'i zai sauka a Kano tunda aka zagi waliyyiyai.

Amma yanzu an taba Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam, shiru kake ji, wasu ma sabida tsabar bakin jahilci da rashin sanin meye martaba da Darajar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam, mune ma masu laifi a wajensu, sabida muna daga maganar, a cewarsu, wai sai dai mu yiwa wanda sukai zagin adduar shiriya. Wallahi karya ne! Hatta 'Ya 'yanmu da jikokinmu sai mun basu labarin cewar 'yan Tijaniya sun zagi Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam a unguwar Makwarari a Kano.

Muna kuma kara tunasar da hukumomi cewar, wallahi wannan maganar ba zamu yi shiru ba, matukar bamu ga an yankewa wadannan zindikai hukunci ba, In sha Allah kotu ta sake su tace basu sabawa dokar kasa ba. Anan ne zasu san cewar ba gata sukai musu ba, Wallahi Darajar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam tafi komai a wannan rayuwa. Rayuwarmu fansa ce gareka Ya Rasulullah!

YASIR RAMADAN GWALE
27-05-2015

No comments:

Post a Comment