Sunday, May 17, 2015

Allah Ka La'anci Wanda Ya Taba Martabar ManzonKa SAW


MARTABAR MANZON ALLAH SALLALLAHU ALAIHI WA SALLAM 

Ya Allah muna rokonka da sunayan ka tsarkaka madaukaka,  Ya Allah kaine kace ku roke ni zan amsa muku! Ya Allah ina me kaskantar da kai a gareka, Ya Allah Kada ka kama mu da laifin da wawayen cikinmu suka aikata musamman na zagi da aibata ManzonKa Sallallahu Alaihi Wa Sallam. Ya Allah kayi dadin tsira a gareshi da Sahabbansa da Alayensa, Alu Aqeel, Alu Abbas, Alu Jaafar da Alu Alee. Ya Allah an cutar da mu da aibata ManzonKa Sallallahu Alaihi Wa Sallam, Ya Allah ka nuna mana misalin kudurarka akan wadannan batattu. Ya Allah ka gwada musu darajar Annabinka tafi duniya da abinda ke cikinta. Ya Allah ka watsa aniyarsu, Ya Allah Kada ka basu dacewa da sabati a cikin dukkan lamuransu na rayuwa. Ya Allah ka faranta mana Rai da saukar musu da masifar da tashin hankali akan abinda suka aikata na zagin AnnabinKa,  fiyayyan Halitta Baban Fatima kakan Hassan Da Hussain Sallallahu Alaihi Wa Sallam. Bi Abi Anta Wa Ummi Ya Rasulullah! 

Yasir Ramadan Gwale 
17-05-2015

No comments:

Post a Comment