Monday, May 18, 2015

Barranta Daga Wannan Mutumin Da Ya Zagi Manzon Allah SAW Kadai Ba Zai Wadatar Ba


BARRANTA DAGA WANNAN MUTUMIN DA YA ZAGI MANZON ALLAH SAW KADAI BA ZAI WADATAR BA 

Idan har wani wanda ba Musulmi ba zai zagi Manzon Allah ko ya zana hotonsa, hankalin al'ummah ya tashi, a farwa wadan da basu san hawa ba basu san sauka ba, da sunan nuna bayar da kariya ga Manzon Allah SAW. Wannan shi ne lokaci mafi dacewa da al'ummar Musulmi a Najeriya ya kamata su misali akan Musulmin da ya zagi Manzon Allah SAW, domin isar da sako ga wadan da ba Musulmi ba da suke tunanin taba mutuntakar Manzon Allah SAW, mu nuna misali akan wannan Zindiki ta hanyar aiwatar da hukuncin da Shariah ta tanada. Wallahi martaba da kimar Manzon Allah tafi duniya da abinda ke cikinta. Zartarwa da wannan Mushrikin hukunci shi ne, zai nuna misali ga cikakkiyar soyayyar da muke ga Manzon Allah SAW.

Wajibin hukumomi ne a Kano su dauki mataki akan wannan mutumin da wadan da suka shirya Maulidin da akai wannan cin mutuncin. Dan uwa Malam Hamisu Nasidi Baban Auwaab, Allah ya saka maka da alheri bisa wannan mataki da ka dauka, hakan ne kuma ya kamaci dukkaninmu, wajen nuna tsantsar soyayya ga Fiyayyen halitta. Sahabbansa, Sallallahu Alaihi Wasallam, sun bayar da dukkan abinda suka mallaka da rayuwarsu saboda shi, sukai mana tsuwurwurin wannan addini har ya kawo garemu.

Dan haka wajibi ne mu tsaya kai da fata wajen ganin an hukunta duk wani mara kunya da yake zaton zai iya taba martabar Manzon Allah SAW ya kwana lafiya. Amma abin mamaki, wasu ko san daga maganar basa son ayi.

Anan a Kano fa wani dan siyasa yace da Malamai da 'yan wasan kwaikwayo duk daya suke wajen koyar da tarbiyya, Malamai suka raja'a akansa akai ta hudubobi akan wannan mutum, sabida an taba mutuntakarsu. To yau gashi, an wayi gari an taba Martabar Manzon Allah SAW, amma wasu na shayin magana akai, sai malamai kalilan suka maida martani akan wannan zindikin.

Wannan batu ba wai kawai a fito ace an barranata daga abinda wannan dan iska ya fada ba shi kenan magana ta lafa, tilas a kaishi gaban alkali ayi masa hukuncin da Shariah ta tanada ga duk wanda ya taba mutuncin Manzon Allah SAW. Allah ka yi dadin tsira a gareshi, Salallallahu Alaihi Wasallam.

Yasir Ramadan Gwale
17-05-2015

No comments:

Post a Comment