Wednesday, May 6, 2015

Takaitaccen Tarihin Imam Shafi'ee



IMAM MUHAMMAD ASH-SHAFI'E

Imam Ash-shafi’e asalin sunansa shi ne: Muhammad Bin Idris Bin Abbas Bin Usman Bin Shafi’e; Abu Abdullah, Ash-shafi’e, Al-qurashi, Al-makki, nasabarsa tana tukewa zuwa ga Lu’ayyu Bin Galib, wato kakannin Manzon Allah(Sallallahu Alaihi Wa Sallam ). 

An haifi Imam Ash-shafi’e a shekarata (150A.H) a garin Makkah, mahaifinsa ya rasu tun yana yaro karami, don haka ya taso ka...rkashin kulawar mahaifiyarsa ne. Imam Shaffi'e ya fara neman ilimi tun yana yaro, ya fara da karatun harshen larabci da kuma wake-waken larabawa har ya tumbatsa a cikin wannan fanni, sannan ya fuskanci karatun fiqihu har ya zamanto jagora a zamaninsa.

Imam Ash-shafi’e ya karanta littafin Muwadda a wajen Imam Malik, ya kuma yi wallafe-wallafe na littattafai da dama, daga cikin mafi shaharar littattafansa akwai: Ar-Risala, da Al-Um, da Al-Musnad, da kuma As-Sunan. 

Imam Ash-shafi’e yana cewa: neman ilimi ya fi sallar nifila, duk wanda ya koyi qur’ani matsayinsa zai daukaka, duk wanda ya karanta hadisi hujjarsa zata yi karfi, duk wanda bai kame kansa ba daga sabon Allah to iliminsa bai masa amfani ba. Imam Ash-shafi’e ya rasu a shekarata (204A.H).

Yasir Ramadan Gwale 
04-05-2015

1 comment: