Sunday, July 28, 2013

SHIN BUHARI NE KE DA MATSALA KO MAGOYA BAYANSA?




SHIN BUHARI NE KE DA MATSALA KO MAGOYA BAYANSA?

Lokaci yayi da ya kamata mu san gaskiyar al’amura dangane da yadde siyasar General Muhammad Buhari take tsakaninsa da mogaya bayansa. Wannan wani batu ne mai muhimmanci a tunanina, kasancewar Buhari mutum daya tamkar da dubu a tsakanin dukkan ‘yan siyasar Arewacin Najeriya ko ma Najeriya gaba daya kwata, wannan ta sanya ya yiwa tsaraiku zarra, a dukkan harkokin sisaya, haka kuma, Buhari ya zama mutum mafi girman tasirin fada a ji a harkokin siyasar Arewacin Najeriya a tsakanin ‘yan Arewa.

Tun lokacin da General Buhari ya shiga harkokin siyasa a kusan gab da zaben 2003, al’amura suke ta wakana dangane da yanayin siyasarsa. A lokacin da Buhari ya kama harkokin siyasa gadan-gadan ya samu dumbin masoya talakawa da magoya baya daga cikin manyan ‘yan Siyasa da kuma tsaffin ma’aikatan gwamnati da tsaffin ‘yan sanda da uwa uba tsaffin sojoji. A takarar da Buhari ya fito ta farko a 2003 da ake ganin cewa babu makawa shine ya lashe zaben aka murde, a wannan lokacin shi ne kusan zamanin da za’a kwatantashi da cewa lokacin da Buhari ya tara dumbin magoya baya a tattare da shi kafin daga bisani al’amura su sauya.

Kamar yadda muka samu labarin cewar a lokacin da Buhari ya fito takarar farko akwai tsaffin manyan sojoji da ake kira “former retired Generals” sama da guda ashirin da biyar (25) wadan da suka rufawa Buharin baya tare da fatan ganin ya kai ga nasara, banda wadan da ake ganin manyan ‘yan siyasa ne wadan da sun isa su yi Magana a sauraresu ko dai a yankunansu ko kuma a cikin jam’iyyar APP da ta rikide zuwa ANPP. Kamar yadda wadan da suke sukar Buhari suke fada cewar kafin shigarsa harkokin siyasa jam’iyyar da ya shiga ta APP mai hamaya tana da kusan gwamnonin jihohin Sokoto, Kebbi, Zamfara, Borno, Yobe, Gombe, Jigawa, Kogi da kuma Kwara; wadannan jihohi tuni jam’iyyar Adawa ta Buhari ta yi musu kwab daya tun a zaben farko na 1999, wanda bayan da aka gudanar da zaben 2003 sai lissafin ya sauya. Domin jihar Kwara da take da mutum mafi girman fada a ji a cikin jam’iyyar APP wato marigayi Alhaji Olusola Saraki da magoya bayansa suka kauracewa jam’iyyar. APP ta yi kokari ta sake ciwo jiha mai matukar muhimmanci wato Kano a zaben 2003 da aka ce Buhari bai samu Nasara ba, a hankali ana tafiya, kida na canzawa rawa ma na canzawa. Inda Buhari ya yi asarar manyan magoya bayan da aka dinga cewa su tafi Allah ya raka taki gona daman su ba na gari bane, kamar yadda abin yake Jam’iyyar Burai ta ciwo Kano kuma ancinye mata wasu.

Jam’iyyar Buhari ta tafka wawar asarar wasu muhimman gurare duk kuwa da zargin da wasu suke yi cewar ba da Allah da Annabi aka kayar da Buhari a wuraren ba, Misali Jihohin Kwara, Kogi, Gombe, Jigawa, Sokoto, Kebbi duk suka koma kasrkashin Jam’iyyar PDP kafin daga bisani jihar Bauchi ta fado hannun jam’iyya mai masara ta Baba Buhari a wancan lokacin. Kamar kulab din wasan kwallaon kafa ne da ya rasa mahara da tsayayyun masu kare gida, dole idan abokin karawarsa ya iyi taka leda yadda ya kamata yayi ta shansa kwallaye babu kakkautawa, kusan haka ne abinda ya faru da Buhari inda aka yi ta zurawa jam’iyyarsa kwallaye duk kuwa da tunanin da ake na cewa yana da zakakuran ‘yan kwallo da tunda suke wasa a baya ba’a taba cin galaba akansu ba.

Da gumu tayi gumu, tafiya kuma tayi tafiya a harkokin siyasar General Muhammadu Buhari shi kansa ya sa-kafa ya tsallake ya bar jam’iyyar tasa ta ANPP inda ya kafa sabuwar jam’iyyar CPC. Kafin fitar Buhari daga ANPP tuni jam’iyyarsu tayi asarar Jihar Bauchi inda gwamnan jihar Isa Yuguda ya fice ya koma PDP. Fitar Gen Buhari daga ANPP ya kafa sabuwar jam’iyyar CPC da yawan masu sharhin siyasa sun ga gajen hakurin Buhari na rashin hakuri a tafi tare a tsohuwar jam’iyyar tasu da take da dumbin magoya baya daga cikin manyan ‘yan siyasa.

Kafin kaiwa zuwa ga kafauwar sabuwar jam’iyyar CPC wadda ta kafu cike da rudani da hayaniya, tuni jiga-jigan mutane wadan da ake musu kirari da cewa idan ka gansu tamkar kaga Buhari ne suka raba gari da Buharin. Mutane irinsu Hajiya Najatu Muhammad, wadda take zaman mace mafi kusanci da Buhari a siyasance ta raba tafiya da tsohon ubangidanta da mutane irinsu Muhammad Adamu Bello da su Brig. Gen Magashi a gefe guda kuma tuni aka raba hanya da irinsu Attahiru Dalhatu Bafarawa inda suka kafa sabuwar jam’iyyarsu mai abarba, wanda shima ya yagi na yaga daga cikin magoya bayan Buharin.

A jumlace baya ga jihohin da jam’iyyar su Buhari suka yi asara sun kuma yi asarar manyan mutane wadan da ko dai suka fito karara suka bayyana basa tare da Buhari ko kuma wadan da suka ja baki suka yi shiru amma kuma sun janye jikinsu a tare da Gen. Buhari, a har kullum masu hikima na cewa shi jari a wajen dan siyasa shine jama’a. Buhari ya rasa mutane irinsu Bukar Abba Ibrahim, Sanata Ali Shareeff, Yariman Bakura, Adamu Aleiru, Ibrahim Shekarau, Bafarawa, Najatu Muhammad da sauransu masu yawan gaske, watakila wasu su zargi wadannan mutane da cewar daman sune suka ciwa Buhari dunduniya a tafiyar ANPP  har suka yi masa hayaki, Allah shine masani.

Bayan da Buhari ya kafa sabuwar jam’iyyar CPC ta samu farin jini tare da karbuwa a wajen talakawa ainun. Jam’iyyar da kusan zaka ce tun da aka kafata da sabbin rikice-rikice ta fara wadan da ake ganin irinsu ne suka sa Buharin ya baro tsohuwar jam’iyyarsa ta ANPP, kafuwar CPC ke da wuya mutane masu bukatar kashin kansu suka dinga yi mata tururwa suna kunno kai ciki, da nufin samun albarkacin Buhari dan kaiwa zuwa ga madafun iko a matakai daban-daban, wanda wannan yana daya daga cikin abubuwa da suka dagwalgwala tafiyar CPC a kusan galibin jihohin Arewa, misali a Kaduna kowa yasan cewar Hon Sani Sha’aban shi ne kusan mutum na farko da zaka lissafa a matsayin na hannun daman Buhari, wanda saboda kaunarsa da Buhari yake sai da Buharin yaki halartar gangamin kaddamar da dukkan ‘yan takara na CPC a jihar Kaduna amma ya halarci gangamin kaddamar da takarar Sha’aban, daga bisani tafiya bata yi nisa ba aka nemi Sha’aban aka sara ya sulale yabar CPC.

Haka kuma, a jihohi irinsu Kano da Katsina da Bauchi da Taraba da Bauchi aka dinga samun rikicin da ya hanawa jam’iyyar wani katabus da zai kaita ga iya kaiwa zuwa ga samun Nasara, duk wannan an zargi wasu daga cikin manyan magoya bayan Buharin da haddasa wannan sabatta-juyatta dan a gurgunata tafiyar CPC da Buhari a wannan jihohi.

Wani muhimmin batu anan shi ne yadda Buhari ya kasa gane masoyansa na hakika da kuma makiyansa na zahiri. Eh! Wannan batu gaskiya ne, domin a jihar Kebbi, Buhari ya dauki al’amuran jam’iyyar CPC sukutum ya mikawa tsohon Gwamna Adamu Aleiru wanda da dama daga cikin makusantan Buhari suka ga baikensa, domin ya kasa fahimtar masoya na hakika, daga cikin wadan da suka ja hankalin Buhari akan kuskuransa na danka ragamar CPC a hannun Adamu Aleiru har da tsohon dogarinsa tsohon sarkin Gwandu Jakolo, haka aka wayi gari Aleiru ya kwarewa Buhari baya inda da shi da dantakararsu na gwamna Gari Malam da sauran magoya bayansu duk suka yiwa PDP kome.

Idan kuma ka dauki jihar Buhari ta Katsina suma haka al’amura suka dagule aka yi kiki-kaka tsakanin bangaren Lado Danmarke da ake ganin babu makawa da ya tsaya a tutar jam’iyyar CPC sai ya kai labari, da kuma tsohon kakakin majalisa Aminu Bello Masari. Itama jihar Kano haka abin yake, inda aka ja tunga tsakanin bangaren Muhammadu Abacha da kuma na Jafaru Isa wanda ake ganin idon Buhari akansa yake, da kuma wanda yake ikirarin cewar shine mutumin da aka yiwa CPC rijista da sunansa, kuma ya bata gidansa a matsayin shalkwatarta wato Sanata Rufai Hanga. A Bauchi da Taraba ma haka labarin yake inda akayi ta samun jumurda a tsakanin ‘ya ‘yan jam’iyyar ta CPC. Duk wadannan abubuwa da suka wakana marasa dadi, rana a tsaka Buhari ya janyo tsohon Minister Nasiru Elrufai a matsayin bakaniken Jam’iyyar CPC, abinda watakila zamu iya tambaya, rikicin da Buhari duk da kima da tasirinsa ya gagareshi shawo kansa, El-Rufai zai iya?

Idan kuma, muka koma batun cewa Buhari ya kasa fahimtar magoya bayansa na hakika da makiyansa na zahiri, sai muga cewa rana a tsaka Buhari ya tsinci wasu mutanen da basu sha wata wahala a tare da shi ba, ya ture wandan da aka dauki dogon lokaci tare da su, ya janyo wadannan tsintattun magunan da PDP ce tayi musu dumi suka tsallake ta, misali mutane irinsu tsohon Minister Nasiru ElRufai da tsohon Kakakin Majalisa Aminu Bello Masari da tsohon Minister Hassan Lawal, wadannan mutane Buhari ya fifita bukatunsu sama da na kowa a cikin sabuwar CPC din, a cikin wadannan mutane wanda zaka ce yana gaba da su a wajen Buhari shine Sule Hamma Yahaya sai kuma Injiniya Buba Galadima.

Kwatsam kuma a makon da ya gabata sai muka ji cewa Buba Galadima ya bayyana ficewarsa daga dukkan al’amuran siyasa inda zai koma gefe ya zama dan kallo. Haka kuma, dukkan wanda ya karanta hirar Buba Galadima a jaridar Aminiya kuma ya yi masa adalci zaiga cewar batun fifita su Elrufai da aka tsinta rana a tsaka aka dankwafe su Buban da dasu aka dinga fadin tashin ganin al’amura sun gudana na daga cikin dalilin barin Buban harkokin siyasa. Na taba jin Dr. Aliyu Tilde ya fada cewar idan gaskiya ta shafi Gen. Buhari sai dai mutum ya ja bakinsa ya tsuke dan gudun bakin jini ko rashin fahimta. Haka ma, a wata wasika da Alhaji Abdulkarim Daiyabu ya taba aikewa da Gen. Buhari mai suna HATTARA DAI GEN BUHARI ya ja hankalin Buhari akan yadda ya fifta Sule Hamma Yahaya akan dukkan wani dan siyasa da yake a tare da shi, Alh. Daiyabu ya gayawa Buhari a cikin wannan wasika cewar shi Abdulkarim Daiyabu yafi Buhari sanin waye Sule Hamma, domin yace tare suka yi karatu kuma suka shiga harkokin siyasa tun jamhuriya ta biyu, inda ya tabbatarwa da Buhari cewar akwai kuskuren sakarwa Hamma ragama da yayi, domin kuwa ya tunawa Buhari cewar a lokacin da Buhari yake shugaban kasar soja shi da kansa ya kama Sule Hamma ya daure a saboda Sulen ya ci amanar kasarnan, wanda yace Sulen na nan da bakin cikin daurin da Buhari yayi masa, amma duk da haka Buhari ya cigaba da maida Sule Hamma danlele da baya laifi.

Koma dai me ya faru lallai yana da kyau mu sani cewa Buhari ba Allan-Musuru bane, mutum ne dan Adam kamar kowa. Dan haka yana da kyau a tunkareshi gaba da gaba a gaya masa irin abubuwan da suke wakana a kuma ja hankalinsa, duk da cewar yana da masaniyar kusan dukkan zarge zargen da akeyiwa na jikinsa akansa, dan yasan mutane na hakika da zai tafi da su a jikinsa da kuma wadan da za’a yi baya-baya da al’amarinsu. Sau da dama mu talakawa da muke nuna soyayya ga Buhari galibinmu daga nesa ne, bamu san yadda al’amura ke gudana ba, ta yadda soyayya ta rufe mana ido muke ganin dukkan wani wanda zai zargi Buhari to shine bashi da gaskiya! Shakka babu Buhari shine mutum na farko da aka fi kyautatawa zato sama da dukkan wani mahaluki a kasarnan, amma wannan ba zai zama madubin da zai nuna cewar komai na Buharin gaskiya ne dari-bisa-dari ba, dole ne a samu kurakurai masu tarin yawa a tattare da Buhari. Idan duk muka kalli abubuwan da suka faru wadan da na fada da wadan da ban fada ba, sai mu tambayi kanmu Shin Buhari Ne Ke Da Mtsala, Ko Kuwa Magoya Bayansa? Magoya baya anan ina nufin manyan ‘yan siyasar da suke tare da shi ba talakawa Masoya ba.

Fitar Buba Galadima daga harkokin siyasa ta sanya dole a sake kallon al’amuran Gen. Muhammadu Buhari da idon basira a kuma gayawa Buharin inda yake da kurakurai kuma suke da bukatar gyara a gyara, shakka babu, duk wanda yasan yadda mutane irinsu Buba Galadima suka yi kaurin suna ba dan komai ba sai akan Buhari, kuma yaji irin wannan korafi na Buban dole yaji damuwa a ransa, ganin cewar gashi kullum kwanan duniya muna kara tunkarar shekarar 2015 ne, wadda zabenta zai fi dukkan zabukan da suka gabata a baya jan-hankali da daukar ido, amma haka da rana tsaka ana samun irin wannan wawar Baraka, lallai da sake wai ambaiwa mai kaza kai.

Lallai mu sani yakin zaben 2015 yaki ne tsakanin gungun barayi, da kuma masu kaya a gyefe guda da suke son karbar kayansu ko da tsiya ko da arziki, haka kuma wannan yaki, bana wasu tsirarun mutane bane, yaki ne da yake bukatar hadin kan kowa da kowa wajen ganin an fitar da al’ummar kasarnan daga cikin halin kangin da jam’iyyar PDP a mataki na tarayya ta sanya al’ummar kasarnan a ciki.

Daga karshe ina kira ga Gen. Muhammadu Buhari da cewa lallai ne ya fahimci gaskiyar yadda lamura suke, a san abinyi, ba dai-dai bane ana samun irin wannan zogayewar manyan mutane a tare da tafiyar hamayya kuma a ja baki a tsuke kowa ya kama gabansa ace masa Allah ya raka taki gona. Ya kamata Buhari ya sasanta da dukkan wadan da suke ganin anyi musu ba daidai ba, haka kuma wadan da Buhari yake ganin sunyi masa ba daidai ba, suma dole ya yafe musu wajen ganin angudu tare kuma an tsira tare.

Mun san da cewar Buhari talakawa ne a gabanka, amma da dama daga cikin wadan da suke cikin wannan tafiya taka akwai wadan da basu da wata alaka ko ta kusa ko ta nesa da talakawa illa iyaka bukatun kansu, ko kuma wani laifi da suke ganin PDP tayi musu, dan haka suka dawo bangaren Adawa dan su huce haushinsu.

Yasir Ramadan Gwale
28-07-2013

No comments:

Post a Comment