Sunday, July 28, 2013

LABARIN AUREN ALH. ISYAKU DA AMARYARSA NABILA MAI SHEKARU 15!




LABARIN AUREN ALH. ISYAKU DA AMARYARSA NABILA MAI SHEKARU 15!

Watana rana a jami’ar Bayero muna zaune da yamma bayan an tashi daga karatun Hadisi wanda Dr. Ahmad (Qala-Haddasana) yake gabatarwa, a Majalisar su Alhaji Isyaku ne na samu wannan labari, dalilin tattauna wannan al’amari kuwa ya biyo bayan wani Hadisi da Malamin ya karanta akan Aure da zamantakewar Iyali, inda Malam yayi dogon sharhi akan hadisin tare da kawo misalai masu yawa dangane da halin da rayuwar aure take ciki a kasar Hausa, da kuma irin yanayin yadda rayuwar yara ‘yan matan wannan zamanin take.

Bayan da muka zauna ne ake sake tattauna wannan batu na yara kanana, sai aka bijiro da labarin auren Alhaji Isyaku da Nabila ‘yar Alh. Muhammad Ahmad. Wata rana, Alhaji Isyaku suna hira da abokinsa Alhaji Muhammad sai yake bashi labarin cewar shi yana burin auren yarinya mai kananan shekaru dan yana son gwada bata tarbiyya irin wadda yake so ba wadda aka dora ta a gidansu ba, Alh. Isyaku ya baiwa abokinsa labarin tare da dalilai masu kwari da yake son yin wannan aure; ashe maganganun sun shiga kunnen Alh. Muhammad sosai da gaske, yana gama bashi labarin kawai sai yace da shi “to indai haka ne me zai hana ka auri Nabila ‘yar wajena” Nanfa Isyaku yayi jugum yana tunanin irin yadda abokinsa yayi saurin martaba wannan ra’ayi nasa, ba tare da wani bata lokaci ba suka amince dan kulla wannan aure. Alhaji Muhammad yace ina zaton shekarun Nabila ko dai 14 ko 15 bazata wuce haka ba.

Nan da nan, bayan Alh. Muhammad ya koma gida ya kirawo diyarsa Nabila yayi mata huduba akan yadda al’amuran wannan rayuwa suke da maganganu na dattako masu ratsa zukata, bai bayyana mata hukuncin abinda suka yanke shi da abokinsa ba, sannan ya kira mahaifiyarta ya sanar mata irin hukuncin da ya yankewa ‘yarsa; da farko mahaifiyar Nabila ta nuna rashin amincewarta da wannan aure, amma daga bisani Alh. Muhammad ya shawo kanta cikin hikimar Magana da bata labarin yadda al’amura suka dagwalgwale a wannan zamanin, ya kuma tabbatar mata da cewa Nabila zata cigaba da karatu a gidan mijinta, idanma tana tsoron karatun yarinyar zai yanke.

Alh. Isyaku shi kuma yana da Matan aure guda biyu da ‘ya ‘ya mata cikinsu kuwa har da wadda ta shiga Jami’a. shima a nasa bangaren ya sanar da matansa cewar zai kara aure ya kuma gaya musu shekarun yarinyar inda matansa suka hade masa kai akan cewa sam ba zai auro musu ‘yar cikinsu ba a matsayin KISHIYARSU, nan dai yayi barazana irin tasa ya kuma tabbatar musu da cewar ba gida daya Nabila zata zauna da su ba, domin samun saukin kishi, haka nan dai suma suka saduda. Ba tare da dibar wani lokaci ba aka daura wannan aure da mutane sukai ta tsegumi akansa.

Bayan an gama aure amarya ta tare a sabon gidan da mijinta ya gina mata. Kamar yadda yake bisa ga al’ada, idan ango zai kashe daren farko da iyalinsa yakan yi dan cefane na kayan dadi ya shiga da su dakin amarya, shima haka Alhaji Isyaku yayi inda ya hadowa Amraya DANASHA, ya kuma kunna kai cikin dakin amaryarsa, bayan da ya shiga ne ya nemi su yi alwala su yi sallah domin godewa Allah akan wannan aure nasu, suka yi sallah kuwa, suka fara cin kayan dadi Bankararrun kaji ne da lemuka da ‘ya ‘yan itatuwa iri-iri.

Ana haka, bayan sun yi hani’an, sai Alhaji Isyaku ya shiga batu babu kakkautawa, inda ya dauki dogon lokaci yana yiwa Amarya nasihohi da kuma jan hankalinta a matsayin sabuwar matar aure da zata shiga wata sabuwar rayuwa ta musamman. Bayan da ya gama yi mata wannan Nasiha ne, a tunanin Alh. Iysaku ita Nabila yarinya ce yana da kyau a barta ta d’an samu sakewa, kafin ta fara sabawa. Kawai ya cire babbar rigarsa ya gyara wajen da suka ci abinci, amarya na kan gado ta sunkuyar da kai, sannan ya dauki Pillow ya ajiye a kasa kan kafet, ya kashe fitila ya kwanta, ya bar Amarya a saman gado ita kadai!

Can bayan wani lokaci Alhaji idonsa biyu, yana jin lokacin da Amarya ta tashi sadaf-sadaf ta d’an kintsa, a zatonsa kunya take ji shi ya sa take sand’a, dan haka sai ya yi lamo kamar yayi barci, yace yana ji tazo kansa tana lekawa taji ko barci yake, bayan wani kankanin lokaci kawai sai jin yarinya yayi ta zo ta kwanta a kusa da shi kamar mage! Nan zuciyarsa ta raya masa anfa zo wajen… amma duk da haka sai yayi kamar yayi barci, kawai, sai ji yayi an fara kunce masa tazugen wando . . . . . . . . . . . . . . . . .! Alhaji Isyaku yace hankalinsa ya tashi matuqa, domin Nabila bata ji kunyar cewa shi abokin mahaifinta bane, kuma shi yana kallonta yarinya karama kamar da sauranta wajen fahimtar yadda al’amuran aure suke, ashe tunaninsa ba gaskiya bane.

Inda hankalinsa ya tashi, shi ne, tunaninsa yana da yara ‘yan mata guda uku wadan da duk sun girmi Nabila a shekaru, nan fa ya kasa samun sukuni, yana ta sake-saken yadda al’amuran wannan zamani suka kasance haka, yace idan har Nabila yarinyar da bata wuce shekaru 15 ba zata kasa jure dare guda na tarewarta ina ga sauran ‘ya ‘yana su Karima da Shamsiya da Salma da take Jami’ah! Lallai abin ya bashi tsoro ainun.

Wa shegari da ya je gidan sauran matansa, ya kirasu akan cewar ya basu watanni uku su shirya bikin ‘ya ‘yansu uku. Sannan ya kira yaransa yake sanar musu cewa ya basu takaitaccen lokaci kowacce a cikinsu ta fitar da mijin aure, idan kuma ba haka ba kuwa, to su sani acikin abokansa akwai  masu son kara aure!

Ya mai karatu wannan labarin fa ba shaci fadi bane, haka abin ya kasance, illa iyaka kawai sunan mutanan da na sauya. Mu kalli yadda al’amarin Alhaji Isyaku da Nabila ya wakana, sannan kuma mu duba batun da ake na cewa WAI kada ka aurar da ‘yarka sai ta haura shekaru 18 da haihuwa. Lallai da sake! Ai laururar da zata sanya ka ki aurar da ‘yarka a kananan shekaru shine rashin samun miji, amma indai ta samu to aurar da ita shine babban abinda ya dace. Allah ka shiryemu ka shirya mana zurriyarmu da al’ummarmu baki daya.

Yasir Ramadan Gwale  
24-07-2013

No comments:

Post a Comment