Wednesday, February 26, 2014

Uganda Ta Aikata Laifi, Amma Faransa Bata Yi Laifi Ba


UGANDA TA AIKATA LAIFI AMMAFARANSA BATAI LAIFIN KOMAI BA

Kasashen Turai da Amerika suna ta yin Tir da kasar Uganda, bayan da shugaban kasar Yuweri Musaveni ya sanya hannu akan dokar da ta haramta aikata Luwadi da Madigo a kasar, suna ta barazanar yanke dukkan irin taimakon da suke baiwa kasar a saboda wannan doka. A cewarta Uwargida Cathrine Ashton Sakatariyar Harkokin wajen Tarayyar Turai, take hakkin Bil-Adama ne haramta aikata Luwadi da aka yi a Uganda, a fadarta, tauyewa mutane hakki ne, yin irin wannan dokar a irin wannan lokaci, matukar mutane sun zabi kasancewa 'yan Luwadi. 

Haka aka ruwaito Shugaban Amerika Obama yana sukar Shugaba Musaveni da kakkausar Murya akan sanyawa wannan doka hannu da ya yi. Sun ce bai kamata a hana mutane zabin abin da suka yi aniyar yi ba.

Amma kuma, a kasar Faransa, gwamnatin kasar a baya ta ce ta Haramta Sanya Niqabi da hijabi a bainar jama'a. Duk kuwa da cewar Musulmi sunyi Imani da yin Lullubin da zai suturce jiki, kamar yadda Allah ya Umarci Manzon Allah SAW yayi kira ga matan Muminai da su suturce jikinsu. Amma babu daya da yace anci zarafin Musulmi da sanya wannan doka. Suna ta kururuwa da baiwa 'Yan Adam 'yancinsu na yin duk abinda suka ga dama.

Amma duk 'yancin da suke kira, shi ne na aikata Alfasha, da 'yancin namiji ya koma mace, da 'yancin Dan Adam ya koma Dabba, Da makamantansu.

26-02-2014

No comments:

Post a Comment