Wednesday, February 12, 2014

Wani Shaidanin Malami A Najeriya



WANI SHAIDANIN MALAMI A NAJERIYA

A Lokacin da Quraishawa suka fito domin Yakar Manzon Allah SAW da Sahabbansa Allah ya yarda da su, a yakin Badar, duk da Sahabban basu da yawa, basu da Makamai, basu Kware a wajen Yaki, amma saida Shaidan yayiwa Mushrukai ta ke yace dasu:

"لاغالب لكم اليوم من الناس واني جار لكم".

"YAU FA BABU WANDA ZAIYI RINJAYE AKANKU,TABBAS KUMA NI INA TARE DAKU".

Amma bayan Shaidan yaga Malaiku suna sauka daga sama da Makamansu, suna kawowa Mumunai da Manzon Allah SAW taimako, sai ya zura a guje, kuma ya kara cewa dasu: "اني برىء منكم اني ارى مالا ترون اني اخاف الله،والله شديد العقاب".

"LALLAI KAM NI BANA TARE DAKU, DON NI INA GANIN ABINDA BAKWA GANI, NI KAM INA JIN TSORON ALLAH, DON ALLAH MAI TSANANIN UQUBA NE".

Hakika Malaman tafsiri sunce Shaidan yazowa Quraishawa ne a cikin Siffar Mutane, ya yi musharaka da su a cikin Shawarwari da kuma farkon Yakin. In Mutane suka lura duk sanda shaidan zaiyi abu tare da Mutane, to cikin Surar shaidan din yake zuwan musu, domin a Lokacin yafi Sharri da kuma tunzurasu. A yanzu ma muna tare da Shaidan a matsayinsa na Mutum, kuma yana nufin ya zuga Mumunai ya hadasu FADA ko kuma yaga suna Kashe Junansu ko ana Kashe su.

Kowa yasan Ahlussunnah wajen bin koyarwar Manzon Allah SAW a lokacin da wata fitina ko Balai ya taso musu, basa daukar doka a hannuwansu, basa afkawa wani domin zargi ko kuma zato. Wannan yana kara sanyawa Jama'a suna kara Fahimtar Sunnah da kuma mabiyanta, da aikinsu a sarari da fili; ba boye boye.

Lokacinda aka Kashe Sheikh Ja'afar Mahmud Adam Rahimahullah, duk duniya an dauka Mumunai zasu fito da rikici da kuma kone kone da sallawantar da dukiyar Jama'a da kisan wadan da basu san hawa ba basu san hausa ba, sai gashi ko ja'ba babu wanda ya Kashe, balle kuma Dan Adam, tunda ba a san Makasan ba. Yanzu ma an Kashe sheikh Auwal Adam Albani Zaria Rahimahullah ,shima ana zaton za ayi tunzuri a kara kashe Jama'a a zaria, amma dai wannan dai koyarwar ta Manzon Allah SAW bata sanya Jama'a sun dauki doka a hannunsu ba.

Kwatsan aka Kawo Sojoji cikin Zaria don kawai suna zaton Mumunai zasuyi Rikici, shima basu sami sa'ar yin hakan ba. Ganin haka ne ya sanya wani Shaidani cikin bakar Alkhabba da rawani, Makaryaci kuma Matsoraci ya fito har yana tutiyar wai Salafawa sun san wanda ya kashe Albani, tsoro ne kawai suke ji suka ki fadan makasan. Burin wannan Sahi dani, shi ne, Mutane su tunzura su fito rikici karnukan Gwamnati su kara hallakasu, sai kuma ya fake da cewa wai shi yasan ko suwaye, kuma zasu fito su fadesu.

1-Abin Tambaya ta yaya ya san haka din?

2-Ko don haka mukaga duk sanda Za'a kama Makamai an shigo dasu Najeriya sai aga 'Yan Shi'a ne, kuma ba ayi musu Komai ba?

3-Yana so yace dama yasan za'ayi Kisan kawai fadane yaki yi, ko kuma sai bayan Kisan aka sanar dashi ko su waye suka yi?

4-Su waye Jami'an Tsaron farin Kayan da suke bashi labari kamar yadda yake cewa???

5-Hakika a fili yake a SOKOTO munga 'Yan Shi'a sunyi kisan kai, kuma Hukumomin Nigeria sun fito dasu wai da tutiyar rashin cikakkiyar shaida (Beyond Reasonable Doubt), amma kuma har yanzu Jama'a basu manta da wannan ba. Dan haka, Ahir Hukumomi suka maida wasu Mutane 'Yan Mowa, wasu kuma 'Yan Bora, domin Hukomomi su bada Tsaro ga wasu, da kuma suka ga abin ya bada Mamaki,s ai kuma suka fito suna neman Wawantar da Mutane. Idonmu a bude yake,muna Karatu ko da wasali ko ba wasali, don haka muna fadake muna ankare muna kuma fadakarwa.

Hattara muke so Hukuma da Sauran Jama'a suyi akan wannan rikici da Wannan Shaidanin Malamin yake Kokarin kawowa a Kasar nan. Allah yasa masu hakkin daukar mataki sun ji,kuma suna gani.

Yasir Ramadan Gwale
12-02-2014

No comments:

Post a Comment