Sunday, February 9, 2014

RE: Ko Shugaban Kasa Bai Isa Ya Gina Coci A Jami'ar Bayero Ba - Galadiman Kano


RE: KO SHUGABAN KASA BAI ISA YA GINA COCI A JAMI'AR BAYERO BA- Galadiman Kano

Jiya na tuntubi makusantan Masarautar Kano dan tabbatar da gaskiyar wannan labari, kuma Alhamdulillah, an tabbatar da cewa wannan al'amari na shari'ar da kungiyar CAN ta kai karar fadar Ma Martaba Sarki akan rushe ginin cocin da aka fara a cikin jami'ar Bayero gaskiya ne, sai dai a yadda aka bada labarin akwai karin gishiri akansa.

Abu na farko dai Mai Girma Galadiman Kano Alh. Tijjani Hashim ya kai ziyarar gani da ido a wajen da ake gina wannan coci a cikin BUK, amma bayan barinsa wajen babu jimawa wasu suka sauke ginin Cocin amma ba Galadima ne ya basu umarnin yin hakan ba. Daga baya labari ya je wajen Galadima cewar ya sanya an rushe ginin cocin, Mai Girma Galadima ya fusata yace, yaga uban da zai gina cocin a BUK ko za'a gina sau goma sai ya sa an rushe sau goma tunda abin rashin kunya ne. Ya kuma kalubalanci duk wanda yake shakka akan haka, ya kuma ce a fara baiwa Musulmi damar gina Masallaci a jami'ar Fatakwal da Nsukka da sauran jami'o'in kudu kafin su bayar da dama a Kano.

Dan gane da batun Shari'ar kuma, kotu ta zauna har karo biyu ba tare da bayyana wakilan Mai Martaba Sarki ba, kamar yadda su CAN suke karar Mai Martaba Sarki akan Zargin Masarauta ta sanya a rusa ginin cocin, inda suke ganin taya za'a ce ana karar wasu amma sunki bayyana a gaban kotu kuma sun ki turo wakilansu. Wanda tun farko da aka nemi mai Martaba Sarki akan ya bayar da Iznin gina cocin, ya shaida musu cewar ba shi da hurumin a cikin jami'ar Bayero da ya shafi wannan aiki.

Sannan kuma, batun cewa Sakataren Gwamnatin Tarayya ya wakilci Sarki a kotu nan ma ba gaskiya bane, hasalima shi Dr. Anyim su ne suke daurewa CAN gindin samar da cocin. Haka kuma, batun cewar dukkan alkalan kotun da Babbar Mai Shari'ah ta kasa Maryam Aloma Mukhtar su gurfana a gaban Mai Martaba Sarki, wannan ma akwai zukale, fadar Mai Martaba Sarki ta bukaci ganin Justice Maryam Aloma Mukhtar zuwa fada a matsayinta na 'yar Kano. Tun cikin Shari'ah ita Kotu ta bukaci a warware wannan al'amari a wajen Kotu.

Yasir Ramadan Gwale
09-02-2014

No comments:

Post a Comment