Tuesday, February 11, 2014

Matsalar Shi'ah Ta Su Wa Ye?


MATSALAR SHI'AH TA SU WAYE?

Kusan da dama daga cikin mutane ba su fahimci meye gaskiyar al'amari game da Shi'ah ba. Wa su da dama suna kallon mun cika matsawa da muke yawan magana akan 'Yan Shi'ah, kuma sau da dama, sukan kalli cewar Matsalar Shi'ah ta 'Yan Ahlussunnah ce su ya su! Da daman mutane wadan da basu san komai game da Shi'ah ba haka suke kallo, a saboda haka ne, suke ganin matsantawa ne, zafin Addini ne ya sanya muka cika yin magana akan Shi'anci, dan haka, duk wani Malami ko mai isar da sako da yin Da'awa da zai yi magana akan Shi'ah sai a dinga yi masa kallon ya cika zafin kishi addini, sau da yawa sukan kafa hujja cewa, ai 'yan Shi'ah Musulmi ne, dan haka abar kowa ya yi abinda yaga dama ko ya fahimta a matsayin addini. Masu irin wannan fahimtar a cikinmu suna da yawa, sai dai sau da yawa nakan yi musu Uzurin rashin sanin meye Shi'anci yake dauke da shi.

Matsalar 'Yan Shi'ah ba ta 'yan Salafiyyah/Wahabiyawa/Izala da duk sunan da aka kiramu ba ce, Al'amarin Shi'ah  batu ne da ya shafi Musulunci gaba daya. Domin dukkan Musulmi na hakika sunyi Imani da cewar garin Makkah nan ne ALKIBLAR Musulmin Duniya gaba daya, kuma Makkah nan ne, inda duk Musulmin Duniya suke haduwa dan yin daya daga cikin Ibadu mafi girma a cikin rukunan Musulunci, wanda a bayyane take cewar a tsarin Shi'ah  babu wani abu da ya yi kama da cewa Makkah ko Ka'abah ita ce alkiblarsu, suna ganin Karbala, nan ne birnin mafi tsarki duk duniya, kuma nan ya kamata Musulmi su maida hankali don ya zama Alkibla. Wannan bayyanannen al'amari ne, domin duk wanda ya ji abinda Shugaban Iraki Nuri Maliki ya fadi a yayin bukukuwan Arba'in da Ashura zai gasgata hakan, ko da bai bibiyi ainihin meye Shi'anci ba. Wannan fa, da kansu suke fada, cewa biranen KARBALA da NAJAF sune birane mafiya tsarki duk duniya, suna ganin MAKKAH da MADINA birane ne da suke dauke da Najasa da datti. Wal'iydhu Billah!

Dukkan Musulmi na hakika da ya Yarda da manzancin Annabi Muhammada Sallalahu Alaihi Wasallam, ya sabawa 'Yan Shiah, ya san karya ce kafirci ne, ba Musulunci bane. Irin wadan nan da suke jingina kansu cewa Musulunci suke yi, su ne wasu ke kiran wai an cika matsanta musu. Bayan a bayyane take cewar mutane ne masu dauke da datti da mugunyar Aqidah da ta ke gurbata addinin Musulunci.

Baya ga wannan, ga aibata da zagin Sahabban Manzon Allah SAW wadan da su ne mafiya daraja a cikin al'ummar Manzon Allah bayansa, suna kafitasu da jifansu da munanan kalmomi, ga zagin Matan Manzon Allah SAW iyayan Muminai. Duk wanda ya tashi a cikin Shiah to akan haka aka tarbiyyantar da shi. 

Dan haka kullum Shi'ah ba su da wani aiki sai rabewa jikin Musulmi domin gurbata musu tunani da sahihiyar Aqidah ta Musulunci. Tayaya zamu bari a dauki yaranmu a kaisu Iran domin yin karatu ko wane iri ne? Wasu na kafa hujja da cewar, mutanan da suka tafi ENGLAND da AMERIKA da FARANSA da CANADA da sauran kasashe shin su me ya sa ba'a ce zasu juye zuwa Kiristanci ba, wanda duk wanda ya yi wannan magana, yana da rarraunan tunani game da sanin meye Shi'ah, ai sauyawa Mutum Aqidah abu ne mai sauki ainun akan sauyawa Mutum addini. A iyakar sanina babu wani mutum da ya je Iran Karatu face sai da ya juye zuwa Shi'anci.

Dan haka, dole muyi Allah wadai da duk wani yunkuri na daukar yaranmu dan kaisu Iran neman karatu ko wanne iri ne, komai tsananin bukatarmu gareshi.

Yasir Ramadan Gwale 
11-02-2014

No comments:

Post a Comment