Sunday, February 23, 2014

Godiya Ta Musamman Ga Gwamnan Kano Rabiu Musa Kwankwaso

GODIYA TA MUSAMMAN GA GWAMNAN KANO RABIU MUSA KWANKWASO

Dole a wannan gabar, mu yabawa Mai Girma Gwamnan Kano Dr. Rabi'u Musa Kwankwaso a bisa nuna mana cewar shi shugaba ne mai sauraron koke-kokenmu, munyi korafi dangane da wata kutunguila da manakisa da aka shirya mana, aka rufe kura da fatar akuya da sunan taimaka mana. Ba shakka, mun yabawa Gwamnan akan yadda ya nuna mana shi mai sauraran al'umma ne, irin haka muke fatan Shugabanni su kasance masu bibiyar ra'ayoyin al'umma.

Tun bayan da aka ce Jakadan Iran a Najeriya ya kaiwa Gwamna ziyara a masaukinsa dake Habuja, ya yi tayin baiwa Yaran Kano tallafin yin karatu a kasar 'Yan SHIAH ta Iran masu bautar son zuciya, masu zagin Sahabban Annabi Sallallahu Alaihi Wasallam da Iyalansa da kafirta Musulmi, muka kasa samun nutsuwa akan wannan makircin da aka so yi mana.

Alhamdulillah, munyi korafi, mun nuna rashin amincewarmu ga wannan shiri na daukar yaranmu don a kaisu Iran karatu, mun bi dukkan hanyoyin da suka halatta a garemu wajen jan hankalin Mai Girma Gwamna wajen nuna masa irin mummunan hadarin da yake tattare da wannan yunkuri na daukar mana yara a kaisu su koyo Zagin Manyan bayin Allah da Iyalan Gidan Manzo da sunan karatu.

Mai Girma Gwamna yaji kukanmu, ya kuma gamsu da irin hadari da mummunar aniyar da aka kudunduno ake son shiryawa al'ummar Kano. Muna nuna farincikinmu da karyewar wannan mummunar manufa ta Farisawa masu bautar son zuciya. Babu shakka, wannan wani al'amari ne mai girma da zamu yiwa Allah SWT godiya a kai. Tare da rokonsa ya karemu, ya kare jiharmu daga dukkan wani makirci da makida irin ta 'Yan SHIAH masu shigo da muggan makamai suna jibgewa a unguwar Bompai dan sanya tsoro da firgici da halaka dubban al'ummar Kano babu gaira babu dalili.

Muna rokon Allah da sunayansa tsakaka madaukaka, Ya Allah ya karemu daga dukkan masu shirya mana sharri, ka mayar da sharrinsu a garesu, Ya Allah ka shiryar da shugabanninmu shiriya ta gaskiya, ka basu ikon fahimtar gaskiya tare da karbarta da kuma aiki da ita. Allah ya sakawa Gwamna da alheri. Allah ya taimaki Jihar Kano.

YASIR RAMADAN GWALE
23-02-2014

No comments:

Post a Comment