Thursday, February 20, 2014

Abinci



ABINCI: Ko tantama babu, cewar ABINCI jigo ne a zamantakewar Aure da Iyali, ABINCI yana sanya farinciki a zukatan iyalai matuka gaya, sannan rashinsa yana sanya bakin ciki da damuwa. Alkhairan da suke tattare da Aninci suna da tarin yawa wanda kowa zai iya yin bayaninsu, misali da abinci ne gabbai ke bubbuga gangar jiki kan wanzu darajarta kan karu, abinci kan sanya Nishadi da walwal. Haka kuma, sharrin da yake tattare da rashin abinci yana da tarin yawa, misali rashinsa kansanya yunwa da da kanjamewa da cituttuka, kai rashin abinci kan sanya wasu zautuwa.

Yanzu ya zaka iya kwatantan farincikin da yake zuciyar wannan yaron? Me ya sanya shi wannan farinciki mabayyani? Amsar ita ce ABINCI. Amma sai dai Kash! Abinci fa yana wahalar da mu kwarai da gaske, duk fadi tashinmu bai wuce na ABINCI ba, kowa ka gani a ko ina yake babu abinda yake sai neman ABINCI. Ba shakka ABINCI damuwarmu ne sosai.

Lallai yana da kyau mu sani cewar, duk ABINCIN da zamu ci a cikinmu dan jin dadi ko dan Larurar yunwa, to kodai ya zama alheri ne garemu dan ya tsurar da tsokokin jikinmu idan ya kasance Halal ne a garemu. Idan kuwa ya kasance ABINCIN da muka ci Haram ne to babu shakka mun ciwowa kanmu Nadama da tashin hankali.

Lallai wajibinmu ne, mu sanya farin ciki a cikin zukatan Iyalanmu da 'yan uwanmu ta hanayar ciyar da su Halal. Ya Allah ka ciyar da Mu Halal ka shayar da Mu Halal.

20-02-2014

No comments:

Post a Comment