Saturday, December 15, 2012

UMAR LAWAN MUHD: Gwarzona Na Shekara A Shafin Facebook (2)


UMAR LAWAN MUHD: Gwarzona Na Shekara A Shafin Facebook (2)
Da sunan ALLAH mai gamammiyar Rahama, mai gamamman jin kai, tsiranSa da AmincinSa su kara tabbata ga baban fatima Annabi Muhammad Salallahu Alaihi Wasallam. Ina shaidawa babu abin bauta bisa gaskiya da cancanta sai ALLAH kuma shi ya aiko mana Manzon ALLAH da sakon musulunci.

Kamar yadda ya gabata a fitowa ta farko, na zabi Malam AbdulQadir Muhammad Bello ya zama gwarzo na daya, kuma wannan munasaba ta kama na zaben gwarzo na biyu. Alhamdulillahi na sake lalubawa da kuma yin nazari akan wannan bawan ALLAH Umar Lawan Muhd. Hakika shima kamar Malam AbdulQadir yana kokari babu dare babu rana wajen ganin ya shiryar da mutane suwa ga hanayar ALLAH karkashin koyarwar Salafussaleh.

Hakika duk mai bibiyar sakonnin da suke fitowa daga turakar wannan bawan ALLAH a shafinsa na facebook zai gasgata ni. Yana da himma da kwazo ainun wajen ganin ya isar da sakon ALLAH zuwa ga ‘yan uwa. Ina bibiyar kusan dukkan sakonnin da wannan bawan ALLAH yake fitarwa ta shafinsa. Na bibiyeshi a lokacin da yake kawo tarihin sahabbai khulafa’urra Shidun da sauran Asharatul Mubashshirina Bil jannah, ya yi kokari matuka gaya wajen bayyanawa mutane irin darajar wadannan bayin ALLAH abokan Manzon ALLAH Salallahu Alaihi Wasallam. Bai gajiya ba wajen wannan muhimmiyar karantarwa wadda muke matukar kishirwarta a wannan lokaci, hakika muna bukatar mutane hazikai kuma jajirtattu irinsu wajen kokarin shiryar da mutane zuwa ga hanyar ALLAH ta wannan shafin.

Haka nan, kaima Malam Umar Lawan Muhd, Ina mai yi maka addu’ah ta fatan alheri tare da tawassuli da sunayan ALLAH tsarkaka madaukaka, ALLAH ya sanyawa rayuwarka Albarka, ya kareka daga da-nasani da kuma kasawa. ALLAH ya yi maka jagora a dukkan lamuranka, Ya sadaka da alkhairan duniya da lahira, ALLAH ya ya daukaka darajarka. ALLAH ya amfanar da al’ummar musulmi da rayuwarka.

Ya ALLAH wannan bawa naka Umar Lawan Muhd ka yafa masa kurakuransu wadan da ya sani da wadan da bai sani ba. Ya ALLAH kasa muyi tarayyah da shi acikin Al-jannarka. ALLAH ka karfafeshi ka kara masa juriya da kwarin guiwa, Ya ALLAH kar ka baiwa Shaidan dama akansa.

Daga karshe ina mai kira ga Gwarzona Malam Umar Lawan Muhd da ya zage dantse ya kara kokari akan kokarin da yake da shi, haka kuma Ina mai yiwa kaina da kai da sauran ‘yan uwa Nasiha da muji tsoron ALLAH acikin dukkan lamuranmu, kuma mu dogara ga ALLAH a cikin dukkan lamuranmu, Lallai ALLAH mai rahama ne mai jinkai, kuma maji rokon bayinSa ne Subhanahu Wata’ala. ALLAH ya hada fuskokinmu a Al-Jannah baki daya.

Yasir Ramadan Gwale

No comments:

Post a Comment