Monday, December 17, 2012

SUWAYE SUKE KOKARIN RURA WUTAR RIKICI A AREWA?


SUWAYE SUKE KOKARIN RURA WUTAR RIKICI A AREWA?

Tun bayan da gwamnan Taraba Danbaba Danfulani Suntai yayi hadarin jirgi ya haukace, hankalin shugabannin CAN ya tashi ganin cewar babu makawa sai Taraba ta kubuce musu wanda kuma har Abada bazata dawo ba.

Sannan da abunda ya faru na mutuwar Gwamna Kaduna Patrick Ibrahim Yakowa kusan wannan shine abinda yafi tayar musu da hankali da rikitamusu lissaf
i, domin wata babbar dama ta kubuce musu.

Kwatsam sai gashi mun wayi gari Gwamnan Benuwai da kansa ba aikeba yana maganganu da zasu haifar da rashin zaman lafiya a kasarnan. Wannan ko shakka babu yana kara bayyana irin mugun nufin shugabannin CAN akan Musulmin Arewacin Najeriya.

Tun suna turo kana nan mutane suna maganganu na tashin hankali har aka fara jin limamancoci da kansu suna wa'azin Takalar fada. Har ta kai yanzu shugabanni da kansu zasu fito suna maganar irin wadda Susuwam yayi wannan ko shakka babu yana kara bayyana cewa lallai suna da mugun kulli a tare dasu.

Alhali mun san Tunda muke a Arewa kullum kiristoci ne suke takalar musulmi da tashin hankali. Rikicin addini na farko wanda Rabaran Abubakar Bako ya yi wani wa'azin takalar musulmi a 1989 inda ya yi maganganun batanci ga fiyayyan halitta, wata dalibar Jami'a ta nuna damuwa, wannan ta sanya aka samu rikici a Kafanchan aka kashe Musulmi da dama.

Sannan bamau manta da lokacin da shugabannin kiristoci suka yi kokarin takalar Musulmi 1991, na kokarin kawo wani Pasto dan kasar Jamus Rein Hart Bonkey ya yi wa’azi a Kano. Inda aka ce zai zo ya tayar da guragu kuma ya bude idanun makafi, wannan ya tayar da kura sosai.

Haka kuma, a cikin shekarar ta 1991, a Tafawa Balewa, Sayawa kiristoci suka yi wa hakimin Lere, Malam Abubakar Bawa kisan gilla; duk da kasancewrsa tsohon da ya haura shekaru 80. Kotu ta samu jagoran wannan ta’asa; Mr. Kyauta (wanda ake wa lakabin Kyankyaso), da laifi ta daure shi. Wanda wannan shine rikici na farko da ya hana Tafawa Balewa zaman lafiya har yau dinnan Rahoton Babalakin ya tabbatar da Hannun shugabannin kirista dumu-dumu wajen shirya kai hari wa Musulmi a wannan gari.

Sannan bamu manta da Katafawan da suka ka kai mummunan hari a kan Musulmi cikin watannin Fabrairu da Yulin 1992; suka kashe daruruwan Musulmi, suka kone gidajensu da dukiyoyinsu. Wanda kotun Kotun Karibi Whyte kirista ta samu Lekwot Zamani da hannu dumu-dumu wajen shirya kai wadannan hare-hare kuma ta yanke masa hukuncin kisa saboda rashin Adalci shugaban kasa na wannan Lokacin IBB yace ya yafe masa wannan mummunar aika-aikar da yayi.

Tun wancan Lokaci har yanzu Kiristoci suna ta kai munanan hare-hare babu kakkautawa a Shandam da Yelwa da Barikin Ladi da Bukur da Jos ta Arewa tun daga 2004 har kawo yanzu ALLAH ne kadai yasan adadin Musulmin da suka rasa rayukansu a Jos har kawo yau dinnan ana ci gaba da kashe Musulmi.

Babu wani rahoton bincike da aka taba kafawa a kasar wanda aka samu hannun Musulmi dumu-dumu da hannu wajen wani tashin hankali. Amma saboda tsabar rainin hankali da Rainin wayo kadangaru irinsu Gwamnan Benuwai Gabriel Torwua Suswam zasu fito suna irin wadannan maganganu na rashin hankali da rashin sanin Inda aka dosa.

No comments:

Post a Comment