Monday, December 17, 2012

GWAMNA GEBRIEL SUSWAM MUGUN KIRISTA



GWAMNA GEBRIEL SUSWAM MUGUN KIRISTA
Gwamna jihar Bunuwai Gabriel Torwua Suswam, ya fada a cikin wata majami'a NKST Church, kuma jaridar Blueprint Newspaper suka buga wannan magana tasa inda yake cewa "Mu hudu ne kadai Kiristoci da aka zaba a matsayin gwamnoni a duk fadin Arewa " Me kake zaton wannan magana take nufi? Arewa Mu Musulmi muke da kaso akalla 75, sannan idan ka dauke jihar Bunuwai da shi Suswam yake Gwamna, sai Jihar Filato nan ne kadai Jihohin da suke da kiristoci da yawa, amma Filtoma muna da yakinin 50-50 muke tsakaninmu da su. Ko kuwa Suswam yana Nufin a samar da Kirista ya zama Gwamna a Jigawa ko Zamfara ne? Wannan ko shakka babu magana ce da bai kamata ta fito daga bakinsa ba a matsayinsa na shugaba.

Sannan ya kara da cewar,"Mutuwar Yakowa a cikin wannan hadarin jirgi ta sanya al'ummar kiristoci cikin wani mawuyacin hali" Shin me Suswam yake nufi akan wannan magana tasa? Shin Ya manta cewa Yakowa Gwamnan Kaduna ne ba Gwamnan Kirista ba? Ko kuwa yana son ya nunawa duniya cewa kulle-kulle aka yiwa Yakowa? Allah mai hikima, Yakowa ya mutu a cikin 'yan uwansa, ba a yankin Arewa ba! na tabbata yau da ace a daya daga cikin Jihohin Arewa wannan jirgi ya rikito da Yakowa sai kaji ana ihu ancika jaridu da hayaniya cewa Musulmi ko kuma a ce Boko Haram ne suka harbo jirginsa, da yake su din makirai ne, suyi amfani da wasu baragurbi suyi Ikirarin cewar dukan jirgin akayi. Amma Allah sai ya sanya abin bai faru a Arewa ba. Alhamdulillah! Da a Arewa ne da bamu san me zai faru ba ya zuwa yanzu.

Gwamna Suswam ya kara da cewa "idan kuma aka lura da mutuwar Gwamna Patrick Yakowa da kuma mawuyacin halinda Gwamna Suntai yake ciki mun zama saura mu biyu kacal kenan" ko kuwa ya manta da cewa Mu mutanan Arewa an kashe mana Sardauna, an kashe tafawa Balewa, an kashe Murtala, an kashe Abacha sannan kuma da Abinda ya faru da 'YarAdua! Shin kana zaton yau wadannan mutane da Kirstoci ne Musulmi suka kashe su Kasar nan zata cigaba da amsa sunan da take amsawa yanzu? Ai da tuni ko dai an fatattaki wasunmu sun koma Nijar ko kuma anyi uwar watsi. Amma da yake mu ba masu son fitina bane lafiyalau kake ji. sannan ya kara da cewa "Rahotannin da nake ta samu na tsaro suna tabbatar min da cewa ni dinnan 'yan Boko Haram zasu kawo mun hari a koda yaushe, a kowanne wuri, a kowanne irin yanayi." "Don haka ina cikin tsananin bukatar addua." Me kaka ke zaton wannan gabar maganar take Nufi? Shin tunda muke mun taba jin Gwamna Suswam a sahun Mutanan da Boko Haram sukewa barazana? Bama kare Boko Hara a cikin dukkan abubuwan da suke aikatawa, domin muna zarginsu duk kullin su Suswam ne da iyayan gidansa. Wannan ko shakka babu Gwamna Suswam ya fada ne domin ya janyo hankalin Kiristoci, dan su kara tsananta kiyayyarsu ga Musulmin Arewa.

Shakka babu Su Suswam sunci nasarar jingina Boko Haram da Musulmi, wanda dukkan mutanan da ake kamawa da daddasa bama-bamai galibinsu kiristoci ne, idan banda Kabiru Sokoto babu wani Musulmi da aka kama da wani laifin kai hari a coci. ko Ali Konduga da aka kama ai babu wani rahoto da ya nuna da hannunsa akan kai hari a coci.Lokaci da zo da wasu zasu kwashi kayansu a hannu insha ALLAH.

1 comment:

  1. hakika lokaci yayi da zamu tashi tsaye mu san irin kiristocin da muke zaune dasu. lokacin mutuwar yar'adua, sunyi murna.... sai kuma yanzu da nasu ya mutu sai suyi zargin mu saboda wasun mu sunyi murna?

    ReplyDelete