Wednesday, December 19, 2012

AL-BISHIR GA JOHN DANFULANI


AL-BISHIR GA JOHN DANFULANI
Ina yiwa John Danfulani albishir da cewa Alhaji Malam Mukhtar Ramalan Yero shine sabon gwamnan jihar Kaduna. Ina kuma sanar da Mista Danfulani cewar a cikin Littafin ALLAH mai tsarki (Al-Qur'ani) ALLAH ta'ala ya gaya mana a cikin sura ta 2, aya ta 26 cewa Mulki nasa ne, yana bayar da shi ga wanda ya so, a lokacin da ya so. ALLAH shine mamallakin Komai kamar yadda ya baiwa Yakowa mulkin Jihar Kaduna a lokacin da babu wanda ya zata Haka ya baiwa Ramalan Yero a yanzu.

Manyan Arna kafurai na gaskiya ba 'yan gareji ba irinsu Utba Ibnu Rabi'a babu irin maganganu na batanci da basu yi ba akan Musulunci da Musulmi, amma yau ina suke? Bayan da aka kashe su Sai da manzon ALLAH ya je kan gawarsu, yana yi musu magana "Shin kun gasgata al'qawarin ALLAH ko kuwa" a dai-dai lokacin da suka kasance masu nadama. Har sai da Umar Bin Khattab ya ce da Manzo Ya Rasulillah yaya kake magana da mutanan da suka mutu, Manzon ALLAH Salallahu Alaihi Wasallam ya shaida masa ko kai baka fisu jin abinda nake fada ba.

Dan haka Mista Danfulani ku sani me aukuwa ce ta auku akan Yakowa kuma ta katse masa hanzari kamar yadda komai tsahon Lokaci sai ta auku akanmu gaba daya. Yanzu kuma mun kara fahimtar mugun Nufinku akanmu, ko ku zargi Mataimakin Shugaban kasa Namadi Sombo ko Kada ku zargeshi babu wani abu da zai faru face mukddari ne daga ALLAH Ubangijin Halittu, Tsarki ya tabbata a gareshi, Subhanahu Wata'ala.

No comments:

Post a Comment