Sunday, January 25, 2015

"Malam Yasir Wallahi Zan Zabi Malam Takai Saboda Kai"



"MALAM YASIR WALLAHI ZAN ZABI TAKAI SABODA KAI"

Jiya wani dan uwa aboki kuma amini ya shaida min cewa wallahi shi zai zabi Malam Saluhu Sagir Takai ne saboda ni. Ya shaida min cewa shi baya PDP amma albarkacina zai zabi Malam Salihu Takai. Ba shakka wannan magana ta faranta min Rai na kuma ji dadinta matuka. Wannan dan uwa ya nuna min kauna kuma yayi min kara, Allah ya saka masa da alheri ya barzumunci da kauna.

Ya Allah muna rokonka da sunayanka tsarkaka madaukaka. Ya Allah ka baiwa Malam Salihu Sagir Takai Gwamnan Kano. Allah ka sa mulkin ya zamar masa sila ta budewar kofofin alheri a jihar Kano baki daya. Ya Allah mun kyautata zato a gareka, kai mai ji ne mai kuma amsawa ne. Allah kaine kace mu rokeka zaka amsa mana Ya Allah ka baiwa Malam Salihu Sagir Takai Gwamnan kano.

Ya Allah ka sani muna kaunar Takai sakamakon kyawawan halayensa da dabi'unsa na zahiri da suka bayyana a garemu. Allah ka tabbatar da duga dugansa wajen yi maka da'a da biyayya. Allah ka bashi ikon tsare gaskiya da mutuncin al'ummar Jihar Kano.

25-01-2015

No comments:

Post a Comment