Sunday, January 18, 2015

Kuskuren Wasu Musulmi Akan Jaridar Kasar Faransa


KUSKUREN WASU MUSULMI AKAN JARIDAR FARANSA

Nakan ga mutane da yawa na yada wasu hotuna na wadan da ba Musulmi ba, da suka yi maganganu na yabawa tare da jinjina ga fiyayyan Halitta Manzon Allah SAW. Ai a matsayinmu na Musulmi tuni Allah ya bamu labarin waye Manzon Allah a cikin alQuraani, yanzu mu da Allah ya bamu labarin ManonSa Sallallahu Alaihi Wasallam, har akwai wani arne da zamu dinga yada maganarsa dan ya yabi Manzon Allah? Duk abin da wani mushuriki daga Mushirikan wannan zamin zai fada na yabawa Manzon Allah, ba zai amfaneshi da komai ba idan bai yi Imani da shi ba, haka kuma, duk wani abu da zai fada bai kai ABU-TALIB ba. Dan haka, idan zamu yada kyawawan Maganganu da aka fada akan Manzon Allah SAW, mu koma cikin al-qurani muji me Allah yace akan ManzonSa Sallallahu AlaihiWasallam.

Haka kuma, yana da kyau mu sani, da yawa masu yada hotunan wannan jarida suna taimakawa gidan jaridar ne wajen yada hotunan. Ba daidai bane, dan mutum zai yada bayanan wannan Jarida sai ya sanya zanen batancin da sukayi akan fiyayyan halitta dan nuna munin aikin da suka yi. Lallai mutane su kaucewa yada hotunan wannan La'anniyar Jarida kuma a yi ta La'antar jaridar.

Sannana kuma, duk wanda zai La'anci wannan Jaridar lallai ne ya halarto da 'yan SHIAH a cikin la'antar tasa. Domin 'yan SHIA sune suka fara zana hoton Manzon Allah suka nuna shi ya daga hannun Sayyadun Aliyu Ibn Abi-talib a matsayin Khalifa. Mabiya Addinin SHIAH sune suka fara yiwa Musulunci zagon kasa kafin wasu arna suyi. Dan haka babban kuskure ne, mutane su dinga La'antar Jaridar kasar Faransa ba tare da sun La'anci 'yan SHIAH masu zana hotan Manzon Allah SAW da Iayalan gidansa ba.

Muna yin Bakarariyar adduar akan duk wanda ya zana hoto yace Manzon Allah ne, ko waye shi Ya Allah ka tsine masa albarka, Allah ka wulakantashi ka La'anceshi, ka kumbura cikinsa, kasa yayi mutuwar wulakanci. Allah ka wargaza shirinsu da sha'aninsu. Allah kar ka basu zaman lafiya da nutsuwa da kwanciyar hankali. Wannan Adduah zamu cigaba da yinta akan wannan La'ananniyar Jarida da kuma 'yan SHIAH masu zana hoton Manzon Allah da iyalan gidansa.

Haka kuma, wannan ba shi ne dalilin da zai sa a farwa wadan da ba Musulmi ba, da basu san hawa ba basu san sauka ba. Arna irinsu Devid David Cameron da suke daurewa wannan cin fuskar addinin gindi suma mu dinga halarto su muna tsine musu. Allah ya taimaki Musulunci da Musulmi ya kaskantar da kafirci da kafirai.

Yasir Ramadan Gwale
18-01-2015

1 comment: