Thursday, January 1, 2015

ADAMAWA 2015; Mallam Nuhu ribadu Ya Zabi Mataimaki


ADAMAWA 2015: NUHU RIBADU YA ZABI MATAIMAKI

Malam Nuhu Ribadu ya bayyana sunan Habila Istifanus tsohon Shugabankaramar hukumar Ganye a matsayin wanda zai dafa masa a kujerar mataimakin Gwamna. Malam Nuhu Ribadu ya bayyana cewa sai da yayi adduah sannan ya tuntubi mutane masu yawa sannan ya yanke hukuncin zaben Mr. Istifanus, wanda ya bayyana shi da cewa mutumin kirki ne mai tsoron Allah da son gaskiya.

Shugabanni Jam'iyyar PDP na jihar Adamawa da kuma shugabannin yakin neman zaben Malam Nuhu Ribadu sun barke da sowwa da murna yayin da Malam Nuhu yake bayyana sunan Habila Istifanus a matsayin mataimakinsa. Mutane da dama sun bayyana wannan zabin a matsayin wanda ya dace, domin an shaidi Mr. Istifanus da cewa mutum ne mai gaskiya da tsoron Allah gashi da son jama'a da san kawo cigaba mai ma'ana.

Haka kuma, Malam Nuhu Ribadu ya bayyana Mr. Habila Istifanus a matsayin masanin siyasa kuma gogaggen mai ilimi, domin kuwa a cewarsa, yayi digirin kwarewa a jami'ar Base dake kasar Burtaniya. daga karshe Malam Nuhu Ribadu da Habila Istifanus sunyi fatan Allah ya dafa musu a wannan takara, ya jama jagoransu. An kuma yi addaur Allah ya baiwa Malam Nuhu Ribadu nasarar wannan zabe.

01-01-2015

No comments:

Post a Comment