Monday, April 22, 2013

GAME DA BATUN MUSULUNTAR RABARAN PETER JATAU!!!


GAME DA BATUN MUSULUNTAR RABARAN PETER JATAU!!!

Kusan a jiya shafukan facebook da yawa da kuma wall na mutane ya cika da bayanin albishir ga 'yan uwa Musulmi cewa wani kasurgumin fasto da yake a ZARIA jihar Kaduna ya karbi musulunci. Mutane da dama sunyi ta nuna murna da farin ciki game da wannan batu na musuluntarsa. Harma naga wani dan uwa ina zaton sunansa Comrade Yusuf Lawal Amaru ya rubuta wani labari cewa yanzu haka suna wani masallaci suna sauraron karatun Malam Jatau wanda aka ce an sauya masa suna zuwa Muhammad Al'ameen. Anan yana da kyau mu Musulmi mu zama wayayyu ba gidadawa ba, Muna murna tare da maraba lale da duk wani wanda zaiyi Imani da Allah da manzonsa, amma labari irin wannan yana da matukar kyau idan an kawowa mutane shi su yi bincike kafin dorar da shi, ban sani ba watakila mutumin da su Comrade Amaru saka saurari wa'azinsa ko shima sunansa PETER JATAU, amma yana da kyau mu sani Shin waye Rev. Peter Jatau kuma guda nawa ne? Dalili kuwa shine a can shekarun baya a Kano a zamanin Gwamnatin Malam Ibrahim Shekaru wani mutum me wannan suna ya kunno kai da cewa shi me wa'azin addinin kirista ne a kasar Zazzau kuma ya kai matsayin Rabaran amma yanzu ya musulunta, an kaishi wajen manyan mutane a kano sosai harda sarakuna inda suka yi masa goma sha-tara ta arziki, sannan kuma, Freedom Radio suma sunyi wani shiri da shi na kusan sa'a guda. Wannan abun duk ya faru ne a wancan lokacin.

Haka kuma, a lokacin da Kungiyar Izala ta shirya wani wa'azi a Gombe a kwanakin baya an gabatar da wani mutum da aka ce sunansa Rev. Peter Jatau ya karbi Addinin Musulunci, kuma yana son ya gaisa da mutane, a wajen wannan wa'azi aka hawar da Mutumin da aka ce sunansa Peter Jatau kan Mumbari ya yi Magana, mutum ne fari amma ba fari tas ba, a wannan lokacin an hada shi wannan mutum Peter Jatau da daya daga cikin Malamanmu a Kano akan cewa Shi Malamin ya sanya a koyar das hi Peter Jatau Ilimin Addinin Musulunci, sunyi Musayar lambar waya da malamin namu da kuma shi Peter Jatau akan cewa idan suka dawo Kano Jatau zai nemi Malam, da yake shi Jatau din ya bayyana cewa yana zaune ne a Kano, shiru-shiru bayan komawa kano daga Gombe Jatau bai kira Malam ba, balle ayi maganar koyar da ilimin addinin Islama, da malam yaga haka sai ya shiga yin bincike akan shin waye Peter Jatau, a sakamakon Bincikensa ya gano cewar shi wannan mutum indai sunansa Rev. Peter Jatau to ya jima da karbar Musulunci ba wai sabon Musulunta bane, har kuma yanzu da nake wannan rubutu shi Peter Jatau bai nemi Malam akan amanar da aka dankawa Malamin akan cewa zai sanya a koya masa Ilimin Addinin Islama ba.

Kwatsam, kuma, a Zaria ina zaton a jiya sai wannan labari na Musuluntar Peter Jatau ya bulla, sai muka shiga cikin rudani akan shin Peter Jatau nawa ne? Lallai jama'a yana da kyau ayi taka tsantsan akan wannan Mutum Rev. Peter Jatau. Sannan kuma muna kira a gareshi idan zai yi Musulunci to ya tsaya ya yi Musulunci tsakaninsa da Allah. Akwai bayanai masu yawa akansa Idan hali yayi zamu bayyana. Wassalamu Alaikum.

Yasir Ramadan Gwale
23-04-2913

1 comment:

  1. Da Gaskiyar ka. Mutumin da naga ni a video yana kiran kansa Peter Jatau wajen shekarun sa za suyi sitin da doriya, amma rev peter Jatau na ainihin zai ka tamanin a yanzu dan ya girme wa Sheikh Dauda Ajofa shikuma yanzu Sheikh Dauda ya doshi casa in a shekaru

    ReplyDelete