Thursday, April 11, 2013

BA MA KIN SHUGABAN KASA DAN SHI BA MUSULMI BANE, SAI DAI . . .

BA MA KIN SHUGABAN KASA DAN SHI BA MUSULMI BANE, SAI DAI . . .

Ko kadan bama kin shugaba Goodluck Jonathan dan kasancewarsa shi ba Musulmi bane. Muna kinsa ne dan shi ba Adali bane, muna kin mummunan halinsa na zalunci da rashin gaskiya da nuna wariyar yanki da kabila. Ya fifita mutanan yankin da ya fito akan sauran 'yan Najeriya, an daga musu kafa suyi dukkan tsiyataku da mugayan kalamai masu barazana ga tsaro, saboda suna da uwa a gindin murhu. Shugaban kasa ya daurewa cin-hanci da rashawa gindi a gwamnatinsa, idan kai gawurtaccen barawo ne ka iya bayar da cin hanci, sai ka zama abokin tafiyarsu, yana yaudarar 'yan Najeriya, gwamnatinsa cike take da tarin masu zunubi marasa tsoron Allah da kishin kasa.

Ya kasa samarwa da al'ummar Najeriya musamman ta Arewa da cikakken tsaro na lafiya da dukiyoyinsu. Amma kuma abin mamaki duk irin wannan barazana ta tsaro da muke fuskanta ta 'yan ta'adda babu irinta a yankin kudu. Shugaban kasa mugun makaryacine wanda ya daurewa karya da yaudara gindi. Yau tattare 'yan abi yarima a gindinsa suna bashi gurguwar shawara, ya kasa samarwa da al'ummar kasararnan abubuwan da ya alkawarta a lokacin yakin neman zabe, duk inda ka shga Iska ta gurbace!

Wannan mutumin, Shugaban kasa ya kai kasarnan ya baro. Yana ta yawan zuwa kasashen Turawa da Amerika yana yi musu karyar cewa gwamnatinsa tana yin iyakacin kokarinta wajen ganin al'amura sun kyautata, alhali kuma a zahiri kowa yasan babu wasu al'amura da suka dauko hanyar kyautatuwa. A zamaninsa ne mutum zai sace dukiya wajen Biliyan 30 amma a yi masa tarar kudin da bai kai Naira Miliyan ba, wannan shine tsabar zalunci da kaiwa makura wajen iya nuna tsageranci da rashin tsoron Allah.

Shugaban kasa bai dauki mutanan Arewa da wata kima ba. Yana kallonsu da wani irin mugun ido ta cikin wani karkataccen Tabarau. Yana ji yana gani ana ta kashe mutane a jihar Pilato babu ji babu gani. Sannan kuma, ga 'yan ta'adda suna yin yadda suka ga dama an barsu suna cin karan da babbaka. Haka kuma, ambar jami'an tsaro da sunan aikin samar da tsaro da zaman lafiya suna cin mutuncin duk wanda suka ga dama, su shiga gidanka su yi maka wulakanci babu inda zaka iya zuwa ka kai kukanka a share maka wahaye.

Wannan wacce irin shedaniyar gwamnati ce da bata da kishin al'ummarta kokadan. Mutum ya sace dukiyar al'umma amma wannan mutumin yace an gafarta masa wai saboda ya gyra halinsa. Wannan shu'umanci ne da kekashewar zuciya.

Wadannan da wasu tarin dalilai sune suka sanya muke nuna matukar kiyayya ga wannan shugaban kasa. Amma ba wai dan kasancewarsa Kirista ba, Yau idan ya gyara halinsa ya nutsu ya zama mutumin kirki ya tsaida Adalci da daidaito zamu yaba masa tare da bashi cikakken goyon baya. Dan haka munyi shirin fatattakarsa ko da tsiya ko da arziki. Shekara ta 2015 kare jini biri jini zamu ga dan iskan da zai kawo mana tallar wannan mutumin mu zabeshi!

No comments:

Post a Comment