Tuesday, June 9, 2015

Ashe Dogara Ma Ya Kada Femi Babanjamila


ASHE DOGARA MA YA KADA FEMI BABANJAMILA??
Yanzu dai babu ko tantama cewar, Shugabannin Jam'iyyar APC ba su da wani iko akan 'yan majalisun da suka ci zabe karkashinsu, dazu a majalisar Dattawa an Kada wanda jam'iyar ta nuna inda aka zabi Abubakar Bukola Saraki tsohon dan PDP wanda ya shigo APC daga baya, bayan ta gama nuna.
Ya zu ma gashi a majalisar wakilai an zabi sabon Kakakin Majalisar Hon. Dogara Yakubu, wanda shima tsohon dan PDP daga jihar Bauchi, ya shiga APC ne bayan D ta gama nuna. Wannan yake nuna cewar 'yan majalisun guda biyu sun kawo karshen fad'a a jin da Jagoran APC na kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu yake da shi a jam'iyar. Zamu jira muga irin yadda itama majalisar karkashin Dogara zata yi nata rabon mukamai din.
Ko za'a samu jituwa tsakanin Bangaren Majalisar wakilai karkashin Jagorancin Saraki da Dogara da kuma Majalisar Zartarwa karkashin sabon Shugaban kasa. A baya dai mu ga yadda akai zaman do ya da man ja tsakanin Goodluck Jonathan Da majalisar wakilai.
Yasir Ramadan Gwale 
09-06-2015

No comments:

Post a Comment