Saturday, September 20, 2014

Muntaka Abdul-Hadi Dabo


MUNTAKA ABDULHADI DABO: A wannan yammaci na Asabar, a madadin Ni da Zainab muke bin sahun dimbin 'yan uwa da abokan arziki na abokina Malam Muntaka Abdul-Hadi Dabo dan taya shi murnar shiga wata sabuwar rayuwa da baya bai taba yin kamarta ba. Ba shakka daga yanzu har zuwa karshen rayuwar Malam muntaka zai samu sauyi gagarumi a rayuwarsa, domin ya matsa daga inda ya tashi ya tsinci kansa tun kuruciya da samartaka zuwa Magidanci. Ba ko tantama wannan wani sauyi ne mai girma a rayuwa kuma mai ma'ana.

Muna taya su murna da farin ciki da fatan alheri a iya tsahon rayuwar aurensu. Lallai daya daga cikin ginshikin burin rayuwar Malam Muntaka ya cika, fatanmu Allah ya tabbatar da su har karshen rayuwarsu, Allah ya basu hakuri da juriyar zama da juna.
Haka kuma, ina amfani da wannan damar nayi kira ga abokina kuma ango da yaji tsoron Allah ya rike diyar mutane tsakani da Allah gwargwadan iyawarsa, ya sani nauyi ne aka dora masa na kula da kansa da kuma abinda ya mallaka na iyalinsa, shi din zai kasance abin tambaya dangane da nauyin da yake kansa a matsayin magidanci. Ina kira a gareka ka zama mai adalci ga iyalinka a koda yaushe.

Ni da Zainab muna yin addu'ah ta musamman a gareka kai da iyalinka Allah ya sanya alheri ya bada zaman lafiya. Allah ya bada zurriyar dayyiba.
YASIR RAMADAN GWALE
20-09-2014

No comments:

Post a Comment