Tuesday, September 9, 2014

Munir Muhammad Usman


Munir Muhammad Usman: Kani na ne, kuma abokina mun tashi tun muna yara, kwanakin baya ya gamu da jarabawar rayuwa, yayi hadari a bisa abin hawa, har ta kai kuma yau dinnan za'a yi masa aikin tiyata, muna yi masa addu'ar fatan alheri da fatan samun lafiya, Allah ya sa abinda ya sameshi ya zama kaffara a gareshi, Allah kuma ya sa a yi masa fida cikin Nasara. Allah ya baka lafiya Muniru, muna rokon 'yan uwa da su sanya shi a cikin addu'o'insu da bakunansu masu albarka.

YASIR RAMADAN GWALE
09-09-2014

No comments:

Post a Comment