Saturday, September 6, 2014

Boko Haram


Manzon Allah SAW yace, a karshen duniya kisa zai yawaita, wanda yake kisa da wanda ake kashewa babu wanda ya san dalilin kisan. Da yawan mutanan da 'yan Boko Haram suke kashewa basu san me suka yi musu ba aka kashe su, watkila idan da za'a tambayi wani dan Boko Haram din sai yace shima bai san dalilin kisan da yayi ba domin shima sashi aka yi (ba-mamaki). Duk wanda yake zaton duniya zata zauna lami-lafiya to ya sauya tunani, domin acikin al'umma akwai waliyyan Allah mutanan kirki wadan da suke umarni da kyakkyawa kuma su yi hani ga mummuna, kuma akwai waliyyan Shaidan, shi Iblis a koda yaushe waliyyansa yana yi musu mummunar huduba ne, yana kawata musu mummunan aiki har su dinga jin babu komai idan sunyi ko da kuwa sun san cewa abinda suka aikata haramun ne, wannan matakin shi ne na kekashewar zuciya Allah ya karemu. Shi yasa da yawa wasu suna yin zina da luwadi da sata, sun san laifi ne, amma suna ganin kamar ba komai, sun gafala cewa direban da yake jan su Iblis ne. Allah kuma labari ya bamu cewa, yana nan yana jiran kowannemu. Allah ka shiryemu shiriya ta gaskiya.

Yasir Ramadan Gwale
06-08-2014

No comments:

Post a Comment