Monday, March 31, 2014

Abinda Ya Faru A Funtua, Ya Taba Faruwa A Kano


ABINDA YA FARU A FUNTUA

Kamar yadda na ji labari tun jiya, cewa wata makaranta mai suna IDEAL an samu wani Malami ya yi wasu tambayoyinJarabawa da suka hargitsa daliban makarantar, har yau litinin muka ji cewa hautsuni ya tashi a garin funtuwar sakamakon wadancan tambayoyin jarabawa da aka ce wani KWAFA dan hidimar kasa wanda Kabila ne ya yi su. Ga dai tambayoyin kamar haka:

"Mohammed is mentally unbalanced, So you should be ___________ of his behaviour. (a) tolerant (b) unintelligible (c) indefinite (d) illegible

13. Aminatu was ________ and it was not clear to me what she meant. (a) unknown (b) unintelligible (c) indefinite (d) illegible."

Wadannan su ne tambayoyin da aka ce sun fitowa yara a cikin jarabawa. Ina ganin akan wannan tambaya, akwai abu na farko da ya kamata a ce anyi. Ya akamata ace kwamatin tsara Jarabawa (Exams Committee) Na makarantar ya duba tambayoyin kafin sakinsu, domin gudun kar su haifar da rashin fahimta.

Sannan abinda ya kamata ayi a wannan lamari shi ne, bincike ba daukar doka a hannu ba. Yana da kyau a samu shi malamin da ya yi tambayoyin aji me yake nufi. Wanne Muhammad yake nufi? Kuma Wace Amina yake nufi, idan yana Nufin MUHAMMAD NAMADI SAMBO ne da AMINA NAMADI to wannan wani al'amari ne daban, idan kuma kai tsaye ya nuna MUHAMMADU Manzon ALLAH SAW yake nufi, to kai tsaye za'a yanka shi ba sai an jira zuwan jami'an tsaro ba.

Ya 'yan shari'ar Musulunci bata bar mutane haka sakaka ba. Saboda hikimar tace ba'a tabbatar da hukuncin ZINA har sai shaidu duka sunga turmi da tabarya, idan biyu suka gani biyu suka saba ganin biyun farko na to za aiwa biyun farko bulalar Qazafi ko da kuwa abinda suka gani din ZINANCE a zahirinta, amma saboda rashin cikar shaidu sai hukunta su.

Irin wannan ta taba faruwa a Makarantar ACE ACADEMY a Kofar Gadon Kaya ina zaton a wajen 2005 inda wata Malama Kwafa itama ta yi makamantan irin wadannan tambayoyi a Jarabawa. Cikin Ikon Allah Malam Jafar Allah ya jikansa ya kwantar da hankulan mutane akan cewa za ayi bincike dan tabbatar da gaskiyar abinda ya faru.

Haka kuma, a garin Bichi irin makamancin haka ta taba faruwa, inda wani Inyamiri ya shiga kasuwa yana talla ance Inyamurin yana son ya Fadi cewa; NA ANNABI YA ZO KASUWA kasancewar bai iya Hausa sosai ba Sai Ya Dinga Cewa GA ANNABI YA ZO KASUWA, babu bincike matasa suka far masa da duka. Wanda sanadiyar haka aka yi kone-kone da yamutsi.

Haka nan, idan akayi tarzoma kamar yadda kuka sani  a cikinmu ana samun masu fasadi, suje suyi ta'addanci, suyi sata suyi zina har gidan giya suna shiga suna fadin wai an zagi annabi su sha giyar suyi intiqami akan wanda bai jiba bai gani ba. A kone dukiyar wadan da basu san hawa ba, basu san sauka ba. Hakan ba shakka yana aukuwa ne saboda bude damar tarzoma da rashin bincike.

YASIR RAMADAN GWALE
31-03-2-14

No comments:

Post a Comment