Thursday, March 6, 2014

Wa'azi . . .!


WA'AZI: Wata rana Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yana zaune, sai ga wani matashi yazo wajensa, yace da shi Ya Manzon Allah Kayi Min Izni Na Yi ZINA! Sai Manzan Allah SAW ya kauda kai, ya kuma maimaitawa, Manzan Allah Ya Kuma Kauda kai, har sau uku. Daga bisani Manzan Allah SAW ya juyo gareshi, Ya tambaye shi, shin zaka yarda wani ya yi Zina da Kanwarka ko Yarka ko Mahaifiyark ko Matarka? yace a'a, Manzan Allah SAW yace da shi to saboda me kake san yin zina alhali baka san ayi da naka! Hakika Allah SWT ya aiko Manzon Allah dan ya kasance Rahama da Shiriya ga Talikai Sallallahu Allaihi Wasallam. Ba shakka wannan wa'azi ne mai girma. Duk wanda zai aikata zina, ba zai so ayi da nasa ba, kuma wadanda zai yi da su din kannen wasu ne ko yayye koma Mahaifiyar wani ce. Allah ka karemu ka kare zuriyyarmu.

Yasir Ramadan Gwale
06-03-2014

No comments:

Post a Comment