Thursday, March 13, 2014

Dan Sanda . . .


DAN SANDA III: Wata rana muna office wajen aiki da daddare, sai muka samu labarin cewa akwai wasu 'yan fashi sun tare hanya, suna harbin mutane, nan da nan na hada wani squad muka fita farautar 'yan fashin nan a daren. Muna zuwa wajen da aka yi fashin, sai muka tarar cewa, 'yan fashin sun gudu, amma, a kasa ga gawarwakin mutane nan yashe a kasa. Abin da na gani shi ne, wasu daga cikin 'yan sandan da muka zo da su, sun fara lalube aljuhun gawarwakin nan suna kwashe dan abinda yake ciki, sannan wasu kuma suna cire agogunan a hannun gawarwakin. Ban taba nadamar shiga aikin dan sanda ba, sai a wannan ranar. Daga lokacin naji duk aikin ya fita daga raina, har na yanke shawarar barin aikin. Amma cikin kaddarawar Allah wani dan uwa ya yi mun nasiha ya nuna min muhimmancin zama na a aikin ya fi ficewata, domin ko babu komai zan iya kawo gyara idan lokacina ya yi. Wannan magana Malam Nuhu Ribadu ya taba fada a wata tattaunawa da aka yi da shi a kwanakin baya. Dan Sanda abokin Kowa.

YASIR RAMADAN GWALE 
13-03-2014

No comments:

Post a Comment