Thursday, March 6, 2014

RE: Boko Haram


RE: BOKO HARAM: 


Assalamu Alaikum Warahmatullah, Hakika Malam Yasir, naji dadin maganarka akan Boko Haram. Kaga mu da muke Borno da wad'an da matsalar Boko Haram ta ke yankinsu ba muda shakka ko kiris akan cewa Boko Haram ne suke ta'addancin nan, wallahi babu hannun gomnati ko Kungiyar CAN, domin mu muka sansu, ka ganni nan nayi MUQABALA da Shugabansu na yanzu wato SHEKAU a garinmu, kuma na kureshi domin da bakinsa ya furta cewa ilimin BOKO ya halatta ako ina, duk da lokacin naje har Maiduguri ne muyi mukabalar da Muhammad Yusuf amma sai ya kauce ya turo Shekau ya wakilceshi, bayan na kureshi na nemi Muhammad Yusuf akan zan zo muyi da shi sai yace sun gama wa'azi sauran yaki ya rage musu, nan take suka cire list namu da malaman Sunnah kusan 150 sukace sai sun kashemu ciki kuwa, har da Sheikh Ja'afar da Albany da abokina Sheikh Fantami, hakika sun sami daman kashe malamai da dama, hatta nima sun sha bani wa'adin kwana uku uku na kisa, ko tada bom don hallakani; bayan target da suka sha shiryawa akaina Allah yana tsare ni, hatta a wannan Ramadan din da ya wuce sunyi target nawa awurin tafsirina da hanya ta ta zuwa tafsirin sama da sau 5, kumafa su da kansu suna fada, Malam hatta wanda yayi commanding kisan Malam Ja'afar dan Borno ne kuma dan Boko Haram ne, wanda yabar aikin ganduroba ya shiga Boko Haram, daf da fadan 2009 bom yatashi dashi a Maiduguri, don barazanarsu saida aka mayar dani barikin soja da zama amma a wancan lokacin ma har gidana na barikin sun gwada zuwa.

Don haka, mu kam, mun sani su suke wannan barnar tunda ni kaina sun taba mini waya kuma na sansu akan zasu kashe Shugaban Majalisar Malaman garinmu mai suna Sheikh Ibrahim Ndatti kuma haka suka kashe shi din. Kuma, akwai wani Malami ana kiransa Sheikh Ibrahin Gomari Basakkwace ne yana Maiduguri da zama wanda yanzu haka ni nake gudanar da tafsirinsa na Ramadan, tare sukayi kaset na KARSHEN ALEWA KASA da Sheikh Albany Zaria, shima sun kasheshi bayan Sallar Magriba kafin ya shiga gida, wasu suka yita yada jita jitar cewa gomnatine, WALLAHI MALAM YASIR da kunnena nake jin wani dan Boko Haram mai suna USMAN OPIPI amfi saninsa da WAL-JIHAD yake fada a waya wa wata 'yar uwarsa wacce matatace yake gaya mata dashi akaje aka kashe shi Sheikh Gomarin yake cewa sunje da bakar JEEF, kuma bayan dan lokaci kadan sojoji sun kai sumame awani gida a Damaturu da aka tsegunta musu cewa Shekau yana gidan, wallahi ansami bakar Jeef din da bindigogi acikin gidan bayan arcewan shekau din. Shi, wannan, WAL-JIHAD din yataba zaman yari a Bauchi sakamakon boren da sukayi na Boko Haram daga baya suka kai farmaki zuwa gidan yarin suka tsere, daga baya kuma aka sake kamashi yayinda suka kai wata sumame yanzu haka yana gidan yari a Abuja.


Gaskiya duk wanda yake kare Boko Haram cewa ba su bane suke kai wannan hare-haren to bai san ainihin lamarin ba, mutanan nan fa a gabanmu suka fara wannan tayar da hankalin, kuma hatta boma boman da aka tayar a Kano a baya wad'an da sukayi kunar bakin waken 'yan garinmu ne, kuma na san wasu daga cikinsu, domin, kafin suyi kunar bakin waken sai sunyi waya, sun nemi gafarar iyayensu akan za su yi kunar bakin wake ranan kaza, amma ba zasu fadi wurinba sai ya faru aji. Gaskiya idan zamu tsaya muna ta zargin wasu wadanda ba su ba kuma muka barrantar da su 'yan Boko Haram din, wallahi zamu wahala, mu kam tuntuni mun sani. Ya rage namu, wanda zai yarda ya yarda, wanda zai ki yarda yaki, kuma wahala a yi ta shanta. Allah ya kare.


NA SAMU WANNAN SAKON DAGA WANI BAWAN ALLAH A JIYA.

No comments:

Post a Comment