Tuesday, December 24, 2013

Wane Darasi 'Yan Arewacin Najeriya Zasu Dauka Daga Sudan Ta Kudu 2


WANE DARASI 'YAN AREWACIN NAJERIYA ZASU DAUKA DAGA SUDAN TA KUDU? [2]

A lokacin da gwamnatin Sudan dake Khartoum ta ci garin Abye mai arzikin manfetur a shekarar bara waccan inda suka fatattaki sojojin Sudan ta Kudu daga yankin, shugaba Omar Albashir yayi wani abu na ba sabamba, inda ya sanya khakin soja ya yi wata Khuduba a ranar juma'ar da suka samu wannan nasara ya sanyawa Hudubar suna "Juwwa Juba" wato sai sun shiga har juba sun cita da yaki. Watakila irin wannan abin da shugaba Bashir yayi shi ne ya burge Shugaban Sudan ta kudu Silva Mayardit Kiir Mai Malafa, a talatar makon da ta gabata aka wayi gari da harbe-harbe a cikin Birnin Juba kawai shima sai aka ga Shugaba Kiir cikin Khakin Soja yayin taron manema labarai, a inda akai ta mamaki kuma abin ya zama abin zolaya ga shugaba Kiir a tsakanin Jaridun Khartoum.

Mutanan Sudan ta kudu suna zaton idan suka balle daga Sudan shi kenan rayuwa zata zamar musu sabuwa su yi ware-wake, su yi duk irin yadda suke so. Amma ina abin ba haka bane, domin Tun bayan ballewarsu, suka yi ta samun kalubale masu yawa da suka hada da rikicin yankin Abye mai arzukin mai, da hadin-kan-kasa da kuma tsaffin 'yan tawayen SPLM da suka jima da makamai a hannunsu suna yawo, da kuma batun gina kasa da Ilimi da kiwon lafiya da noma da sauransu. Duk da irin wannan kalubale dake gaban Gwamnatin Silva Mayardit Kiir Mai Malafa, maimakon ya hada kan al'ummomin kasar wajen ciyar da kasar gaba, sai ya dabarbarce yayi ta jidar dukiyar kasar yana tarawa a cewar masu hamayya da gwamnatinsa karkashin jagorancin Reak Machar.

Yana da kyau mu sani cewar Mutanan Kudancin Sudan kusan mafiya yawansu sun saba da yaki, kuma sun saba da gudun hijira, dan gabaki dayan rayuwarsu a haka ta taso. Dan haka ne da aka wayi gari da wannan harbe-harbe a Juba tsakanin Dakarun Reak Machar da na Gwamnatin Kiir Mai Malafa, jama'a da dama suka dinga diban tsummokaransu da katifu suna zuwa ofisoshin majalisar dinkin duniya dan samun mafaka. A lokacin da Shugaba Kiir ya tashi yin taron manema labarai ya ambaci sunan tsohon mataimakinsa Reak Machar da cewa shi ne ya haddasa wannan tashin tashi-na, abinda wasu manzarta suke ganin Kiir yayi azarbabin kama sunan Machar, mutumin da a yanzu yake neman goyon bayansa dan dawo da doka da oda. Haka kuma, wani dalili da zai nuna gazawar Gwamnatin kiir shi ne yadda cikin kankanin lokaci aka karbe ikon Jihar Unity da Upper Nile daga hannun gwamnati abinda ya nuna daman can gwamnati ba tada wani tanadi ingantacce na tsaron kasa.

Darasin da masu fatan ganin Arewa ta zama kasa mai cin gashin kanta bayan ta yanke daga Najeriya shi ne, za'a samu tsananin gaba da kiyayya tsakanin Musulmi da Kiristoci a Arewa. A sudan ta Kudu matsalarsu kabila ce kawai, dan haka, lamari ne da ake iya warware shi akan tebur, amma dangane da Arewacin Najeriya batu ne za'ai na addini tsakanin Hausa/Fulani-Musulmi da sauran Kabilun Idoma/Berom/Tarok-Kiristoci da sauran kananan kabilun da suke Arewa. Wannan shi ne abinda zai sabbaba rashin jituwa mai tsananin gaske, abida ka iya kaiwa zuwa ga gwabza yaki, da dama suna ganin Idan mu Arewa muka balle shi kenan zamu tafiyar da rayuwarmu yadda muka ga dama. Sabanin yadda muke a dunkulalliyar Najeriya inda ake kudu da Arewa. Ba shakka sharrin da zai biyo bayan darewar najeriya sai an gwammace inama dai ba'a rabu ba! Akwai illoli masu yawa wadan da darewar Najeriya zata haifar. Dan haka wannan turka-turka ta kasar Sudan Ta kudu take zaman babban Darasi ga 'yan Najeriya musamman mu 'yan Arewa.

Yasir Ramadan Gwale
24-12-13

1 comment:

  1. Malam yasir kayi gaskiya saidai dan gyara kadan a rubutun ka. Kudancin nigeria sune ke bukatar raba kasa ba arewaci ba

    ReplyDelete