Saturday, December 28, 2013

Bayan Tattaki Kuma Sai Me?

BAYAN TATTAKI KUMA SAI ME?

Yanzu dai angama Ibadar da 'yan Shia'h suka yi a Husainiyya dake Zariya da sukawo Tattaki daga gurare masu nisa. Wanda a ranar wannan taro nasu muka jiyo Nuri Maliki Mai Gasa-Burodi a Bagadaza wanda yanzu prime Minister ne na Iraqi Bayan Shahadar Marigayi Saddam Hussein Rahimahullah yana cewa Musulmi su mayar da Alkibla zuwa KARBALA domin anan ne Kabarin Sayyaidina Husain Ibn Ali Ibn Abi-Talib (Radiyallahu Anhu) yake. Shin ko Maliki ya mance da cew
ar Kabarin kakan Husain baban mahaifiyar Husain Annabi Muhammadu Dan-Abdullahi cikamakin Annabawa yana garin Madina Al-munawwarah ne, watakila ko bai sani ba ne. To amma su Masu bakaken kaya na Najeriya da basa iya zuwa Karbala a irin wannan ranar har suma zasu dinga kallon Karbala ne ko kuwa su GYALLESU zasu dinga Kallo yayin da zasu yi tasu ibadar? Dan Allah ku bani labari shin Masu Tattakin nan a kafa suka juyo zuwa mazaunansu ko kuwa ladan zuwa (safa) ya ishesu, ba sai sunyi (marwa) ba suka hawo ababen hawa dan komawa gida? Sannan kuma, bayan da a yanzu suka yi Idin-Ghadir da Idin Ashura sai kuma meye ya rage? Sai naji daga gareku.

Yasir Ramadan Gwale
28-12-13

No comments:

Post a Comment