Thursday, December 12, 2013

Obasanjo Ya Fadi Gaskiya, Amma Mai Zunubi Ne

OBASANJO YA FADI GASKIYA, AMMA MAI ZUNUBI NE

Ba shakka wasikar da tsohon shugaban kasa Obasanjo ya aikewa Shugaban kasa Goodluck Jonathan ya yi bayanai na gaskiya da dattako. Obasanjo saninmu ne ba wani mutum bane mai gaskiya, yana daga cikin ummul haba'isin duk halin da muke ciki na kaskanci da koma baya a kasarnan Musamman yankin Arewa, bamu manta da yadda ya lalata mana tattalin arziki ba ta hanyar amfani da karnukan farautarsa, ya nakastamu ta fannin karfin soja. Ya mayar da mu baya a harkar noma da kiwo da muke tunkaho da shi, a gefe guda kuma ya daga darajar noma da kiwo a yankin kudancin Najeriya. Bamu manta da irin yadda ya yi amfani da murar suntsaye ba ya nakasta da dama daga cikin manyan manoman arewa ba.

Hakika laifukan da Obasanjo ya tafka a wannan kasa ba zasu lissafu ba cikin kankanin lokaci. Anyi kwangiloli na rainin wayo da raina 'yan Najeriya, bamu manta da kwangilar Naira Biliyan 200 da aka sanya Cif Tony Anineh ba, akan gyaran manyan hanyoyin gwamnain tarayya ba, wanda babu kudin babu dalilinsu, kuma babu aikin, bamu manta da badakalar kudin wutar lantarki ba. Da dumbin laifuka da zunubbai da ya aikatawa al'ummar Najeriya duk suna nan rubuce a cikin daftarinmu.

Babban laifinsa mafi muni, shi ne yadda yayi uwa yayi makarbiya wajen shigowa da 'yan Najeriya da haramtacciyar Gwamnati a 2007. Saninmu ne shi ne ya daurewa Marigayi Malam Umaru Musa YarAdua (Allah ya jikansa da rahama) gindi wajen yakai labari ko ta halin-kaka. Shi ne kuma ya daurewa Wannan mugun shugaban kasar gindi wajen dawowa a matsayin magajin Umaru YarAdua. Har yanzu wannan ciwo da miki da Obasanjo ya aikata mana bai warke ba a zukatanmu.

Ba haushe ya yi gaskiya, yace gaskiya ko ta karece a bashi abarsa! Kuma haka addinin Musulunci ya horemu. Ba shakka Duk da waccan balbalcewa da lalacewa ta Obasanjo yayi gaskiya akan abinda ya fada game da yadda Shugaban kasa Goodluck yake tafiyar da harkokin wannan kasa. Masana sun jima da fadin cewa, a tarihi ba'a taba samun shugaban kasar da bai san me yake yi ba, irin wannan mugun mayaudarin shugaban kasar, Azzalumi maketaci, mayaudari wanda baya son al'ummar Najeriya da alheri ko na sisin kwabo. Ya mayar da kasarnan baya ta ko ina, ya lalata komai. Ya daurewa cin hanci da rashawa gindi, ya mayar da aikata zunubbai tamkar Ibada.

Anyi hasarar dumbin rayukan talakawa bayin Allah da basu san hawa ba balle sauka a wannan muguwa Azzalumar gwamnti. Mutane da yawa sun talauce a sanadiyar kona musu dukiyoyinsu a jihohi da dama a Arewa. Barna da ta'adi da wawaso da facaka sun zama sune abinda kowa ke alakanta wannan gwamnati da shi ciki da wajen Najeriya. Ya sace dukiyar kasa shi da wasu tsirarun 'yan iska maciya amanar kasarsu, marasa kishi, sun zamar mana Alaka-kai. Babu shakka dukkan dangin wani kasawa ya tabbata akan wannan shugaban kasa, mugu ne, maketaci ne, Azzalumi ne, 'yan Najeriya birni da kauye sun gaji da wannan gwamnati. Dan haka dole mu yabawa Obasanjo akan abinda ya fada dan gane da wannan shugaban kasa da Azzalumar Gwamnatinsa. Allah ya yi mana canji mai amfani a 2015.

Yasir Ramadan Gwale
12-12-13

No comments:

Post a Comment