Monday, December 30, 2013

Iran


IRAN: Duk wani yunkuri na dakushe tare da rage karfi da tasirin Kasar Iran a yankin gabas ta tsakiya, musamman a kasashen Lubnan da Suriya da Iraqi abu ne da ya kamata ya samu goyon baya daga dukkanninmu. Muna maraba da dukkan wani yunkuri akan haka. Iran ta zama iblishiya a tsakanin kasashen Gabas ta tsakiya, ta hada-kai da Israela ana ta wasa da hankulan mutane dangane da makamin Nukiliya. Suna karfafa Hiz-bola tana kashe mutane a Lubnan, sun kashe Rafeeq Alhariri Rahimahullah, sun kuma kashe Mumammad Shattah. Suna kuma taimakon Bashar Asad dan Ta'adda yana kashe talakawa bayin Allah a suriya. Sannan kuma, sun mayar da Iraqi tamkar wata jiha ce a cikin Farisa ta hanyar bayar da umarni ga karen farautarsu Nuri Maliki dan ta'adda. Muna nuna cikakken goyon bayanmu akan dankwafar da Iran. Ina kuma da yakinin za'a cimma Nasara, dan Allah yana taimakon duk inda gaskiya take komai karancin masu yi mata biyayya. Allah ka rusa duk wasu masu yiwa Addini zagon kasa suna basaja a cikin musulmi.

YASIR RAMADAN GWALE
29-12-2013

No comments:

Post a Comment