Saturday, December 21, 2013

Obasanjo Ne Fa . . . Gwanki Mai Rangwangwan!!!


OBASANJO NE FA . . . GWANKI MAI RANGWANGWAN!!!

Wasikar da aka ruwaito tsohon shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo ya rubutawa Shugaban kasa Goodluck Jonathan ta janyo masa farin jini da yawa a wajen mutane masu saurin manta abinda ya faru a baya. Ba shakka yana da kyau mu tunawa kanmu waye Obasanjo a wajenmu ('Yan Arewa), sannan kuma mu tambayi kanmu, Shin Allah ne ya shiryi Obasanjo? Sannan kuma, halin da muke ciki mawuyaci na koma baya ta fuskar tattalin arziki, da lalacewar harkar ilimi, da koma baya ta fuskar Noma da kiwo, da lalacewar harkokin tsaro da fatara da yunwa da cututtuka da sauransu, wadannan wasu lamura ne da mu mutanan Arewa bama bukatar Obasanjo ya sanar da mu wadannan lamura. Dukkan irin lalacewa da wannan gwamnati ta mai malafa ta yi da kuma gasa mana aya a hannu da ta yi, Obasanjo yana da kamasho a ciki ko mun yaba masa ko bamu yaba masa ba, domin shi ne silar samuwarta.

Kada mutanan Arewa mu yi saurin manta irin kitififi da kitumurmura da makircin da Obasanjo ya shirya mana a baya. Mutumin nan, shi ne fa ya yi dukkan mai yuwuwa wajen mayar da yankin Arewa baya ta fuskar tattalin arziki da karfin soja da ilimin boko da sauransu. Manyan sojojin Najeriya 'yan Arewa masu mukamin General da Brigadier da Major nawa ne suka rasa rayukansu a cikin wani yanayi mai cike da tuhuma a zamanin Obasanjo? 'Yan kasuwa nawa aka gurgunta bayan an kakkarya wasu a Arewa? Ina bankin da Arewa take takama da shi na Bank Of The North? Shin ba Obasanjo ne ya rusa shi ba, dan murkushe tattalin arzikinmu! Shin ba Obasanjo ne ya yi amfani da Kwanturola na Kwastam Jacob Gyang Buba ba wajen durkusar da kasuwannin jihar kano da na Arewacin Najeriya ba, ta hanyar bin mutane har cikin shagunansu ana kwashe musu kaya ana konewa dan tsabar zalunci da keta da mugunta? Shin yanzu har munyi saurin manta irin wannan manakisar da Oban-shegu ya yi mana?

Dukkan zaben da aka yi a baya tun daga 2003 har zuwa 2011 shin ba Obasanjo ne ya yi amfani da karfinsa ba wajen yin kaci-baka-ci ba, baka-ci-ba-kaci! Duk irin wannan shegantaka da tsiyataku da Obasanjo ya yi mana har muna da bakin da zamu yaba masa akan ya rubutawa Shugaban kasa Goodluck wata wasika da babu abin da zata rage na daga irin mawuyacin halin da muke ciki ba. Shin Obasanjo yanzu yana son nuna mana cewa a yanzu shi masoyin 'yan Arewa ne, yana gaya mana manakisar da wannan gwamnati ta shirya dan kashe wasu muhimman mutane? Mutum nawa aka kashe a Arewa da Najeriya baki daya wanda Obasajo ya kamata ya yi bayanin yadda aka yi kisan kuma aka kasa gano wadan da suka yi kisan!

Obasanjo yana shugabancin Kwamitin Amintattu na Jam'iyyar PDP, tsohon mashawarcin kasa ta fuskar tsaro Marigayi Andrew Azazi ya yi bayanin cewar PDP su ne BOKO HARAM, Shin ina Obasanjo yake a lokacin? Ko Azazi yace banda Obasanjo ne? A saboda a wautar da hankalin mutane sai aka ce wai Obasanjo zai je Maiduguri domin sasanta Gwamnatin Borno da 'Yan Boko Haram, a yi wasa da hankulanmu, shin zamu iya gamsuwa cewa babu hannun Obasanjo a cikin duk wannan sabatta juyatta da ake yi ta fuskar tsaro ne? Ba obasanjo ne ya yi uwa yayi makarbiya ba wajen ganin ya daurewa wannan shugaban mai malafa gindi ya tsula dukkan irin tsiyar da yaga dama ba? Bai kamata mu yi saurin mancewa da abin da Obasanjo ya aikata mana ba, har mu dinga yekuwa da sunan cewa OBJ yayi abin kai fitsari da kumfa! Kamar yadda na fada, shin muna bukatar Obasanjo ya fada mana halin da muke ciki, ko ya ce mana za'a kashe mu? Ina kisan da ya yi mana a baya? Shedan ya fadi magana Manzon Allah SAW ya ce abinda ya fada gaskiya ne, amma shi din makaryaci ne, dan haka gaskiyar da ya fada bata tsarkakeshi daga kan batan da yake kai ba; to haka shima Obasanjo.

Obasanjo ya fahimci 'yan Arewa sarai dan haka ya gama rainamu ya yi dukkan irin wasan da yaga dama da hankulanmu. Domin ya fahimci yanzu duk wani wanda zai samu farin jini da karbuwa musamman a wajen 'yan Arewa to ya kalubalanci gwamnatin mai malafa, dan haka ya fito da wannan sigar dan ya mantar da mu abin da ya faru a baya na badakalar da ya tafka a Kwangilar Wutar Lantarki ta Dala Biliyan Goma sha shida ($16B) ya mantar da mu badakalar da su Cif Tony Anineh da su Bode George suka tafka a karkashin gwamnatinsa.

Ni a ganina, wannan wasika ta Obasanjo tana da fuskar silai (mutum ko Doki), Abu na farko shi ne, ficewar Gwamnonin PDP guda biyar babu shakka sun batawa Obasanjo rai, dan bai so haka ba, dan haka bari yayi amfani da wannan dama ya caccaki mutumin da 'yan Arewa suke tsananin kyamata da nunawa gaba, ta hanyar nuna mana cewar yanzu Mulki rabon 'yan Arewa ne, bayan mun san da cewar yayi dukkan abin da zai iya wajen murdewa kundin tsarin mulkin Najeriya wuya dan ya zarce a karo na uku Allah bai nufa ba, ko waccan Tazarce ba 'yan Arewa ya so ya yiwa sata ba? Duk da mun hana shi wucewa ba dan yana so ba, muka zuba masa ido ya zabo mana wanda yaga dama a matsayin wanda zai gajeshi, kuma, muka ce masa "sami'ina wa'ada'na". Dan haka, duk wani sabani da za'a samu tsakanin Obasanjo da Goodluck ko da kuwa OBJ zai halaka mahaifiyar Shugaban kasa ba shakka zasu gyarota a tsakaninsu.

Abu na biyu, Obasanjo ya hango hadarin da yake tunkaro PDP ba mai ruwa bane, hadari ne mai tafe da kura da guguwa da zata yi awon gaba da duk abinda ta samu, dan haka bari ya yi riga malam Masallaci; tunda ya fahimci cewar duk wanda zai yi farin jini a idan APC to ya caccaki shugaban kasa Jonathan, komai lalacewarsa hakan zata bashi kima a wajen APC tunda anyi walkiya yaga wallensu. Ni a ganina wadannan dalilai guda biyu suka sanya Obasanjo rubuta wannan wasika, idan tayi ruwa rijiya, idan kuma tayi fako shadda ce, yasan indai APC ta kafa gwamnati a kalla ya wanke kansa ta hanyar caccakar gwamnatin GEJ da tsinken-tsire, idan kuma abin Allah ya kiyaye GEJ ya kai labari, to babu shakka zai gyarota tsakaninsa da Shugaban kasa, kamar yadda muka hangosu a Nairobi da Soweto suna musabiha cikin annashuwa bayan aikewa da wannan wasikar. Hausawa sun ce a Juri 'Bara Albasa Fara Ce.

Yasir Ramadan Gwale
21-12-2013

No comments:

Post a Comment