Thursday, December 12, 2013

Sheikh Aliyu Harazumi Hausawa


SHEIKH ALIYU HARAZUMI: Ina mai bin sahun dimbin al'ummar Musulmi musamman na jihar Kano da karamar hukumar Gwale wajen nuna alhininmu bisa rashi na Shehun Malami Sheikh Aliyu Harazumi, hakika dukkan mai rai mamaci ne, kasancewarmu a raye babban dalili ne da yake tabbatar mana da cewa Mutuwa na nan tana jiranmu komai tsawon lokacin da muka diba a rayuwa. Mutuwa ita ce mai yanke dukkan hanzarin abin halitta da yake motsi a ban kasa, dole zuciya ta kadu idanu su raurawa hankali ya dugunzuma, a yayin da mutum yayi rashin wani nasa musamman mutum irin Sheikh Harazumi da yayi tasiri a zukatan mutane da yawa. Muna baiwa juna hakuri a bisa wannan rashi, muna kuma tunasar da juna cewa wannan sunnar Allah ce, kamar yadda ya fada a cikin littafinsa mai tsarki cewa dukkan mai rai sai ya dandana radadin mutuwa. Haka nan kowannemu zai riski wa'adinsa, babu tsumi babu dabara a lokacin da wa'adi yayi. Ba shakka a wannan lokacin anyi rashe-rashe na Malamai irin s Sheikhu Na'ibi Sulaiman Wali da Sheikh Isah Waziri da kuma wannan ta sheikh Aliyu Harazumi.

Ya 'yan uwa na masu girma, hakika a rayuwa babu wani wa'azi da yakai mutuwa. Ba shakka mutuwa ita ce Muntaha a rayuwar dan adam, lallai mu nustu, mu fadaka, mu sani, mu ba mazauna bane, yadda muke fadan cewa wane da wane sun rigamu gidan gaskiya, haka muma wataran za'a bayar da labarin tafiyarmu inda babu dawowa, dan haka nake jan hankalinmu da mu jajirce wajen yiwa wannan tafiya Guzuri na tsoron Allah da Imani da kadaita Allah da bauta, tare da yawan Istigfari da Hailala da karatun Al-Qur'ani. Allah ya bamu ikon tafiya, Allah ya rinjayar da kyawawan ayyukanmu akan sikelin ranar Alkiyama. Ranar da Allah ya kirata da sunaye da yawa dan jan hankin bayi na gari masu kadaitashi da bauta. Allah ka jikan mamatanmu, da 'yan uwanmu da malamanmu da dukkan al'ummar Musulmi a duk inda suke a duniya.

YASIR RAMADAN GWALE
12-12-13

No comments:

Post a Comment