Wednesday, November 14, 2012

‘Yan Najeriya Na Wancakalar Da Babbar Dama



‘Yan Najeriya Na Wancakalar Da Babbar Dama

Sau da dama nakan yi mamaki yadda mu ‘yan Najeriya muka cika yawan korafi akan rashin tabuka wani abun kuzo mugani da masu muki suke yi. Kullum muna ta yamadidi da cewa masu mulki idan anzabesu suna komawa su zama ‘yan dumama kujera da amshin shata ga iyayan gidansu wadan da suke zama tsani na hayewarsu kan Dukkan wasu madafun iko.

Siyasa na da muhimmanci ga kowace kasa da take bin tafarkin mulkin dimokaradiyya, dalili akan haka kuwa shine tsarin siyasar demokaradiyya na Baiwa al’umma kasa damar zaben shugabannin ko wakilai da zasu jagoranci al’umma ta Dukkan bangarori na gwamnati, wannan tsari na demokaradiyya ya Baiwa al’ummar kasa damar zaben mutanan da suke ganin sun cancanta da su share musu hawaye domin fitar da su daga halin kunci da masti na rayuwa.

Al’ummar kasa suna bayar da goyon baya ainun wajen ganin sun marawa mutumin da suke da yakin zai share musu hawaye, ya samu kaiwa ga gaci domin yi musu shugabanci ko wakilci nagari. To amma babban kuskuren da al’umma suke tafkawa wajen zaben shugabannin da wakilai shi ne shin sanin tayaya talakawa zasu san mutumin da ya dace su zaba ya shuagabancesu ko ya wakilce su? A lokuta da dama talakawa na korafin cewar sunyi zaben tumun-dare musamman ga wakilai wadanda suke tafiya majalisar kasa su zama ‘ya Aye da Nay.

Talakawa ko masu zabe suna da babbar dama da kusan tun da Najeriya ta komo mulki irin na tsarin demokaradiyya ake ta wanacakali da wannan muhimmiyar damar. Domin tsarin mulkin da yanzu ake neman yiwa kwaskwarima ya yi tanadin cewa duk mutumin da baya yiwa al’umma wakilci na gari suna iya yi masa kiranye ya dawo gida a sake zabe a tura sabon wakili, amma wannan damar muna ji muna kallo ta saraya a garemu, duk kuwa da masu ilimi da muke da su da suka san da zaman wannan ayar doka. Duk mutumin da muka zaba muna ji muna kallo sai ya tafka tsiyarsa har ta tsawon shekaru hudu, ya kudance ya zama hamshakin attajiri cikin ‘yan shekarun da basu kai cikin ‘yan yatsunsa ba.

Mafiya yawan wadan da suke yin korafin cewar sun zabi wakili ko shugaba yaje yana dumama kujera sune matasa. Wanda a hakikanin gaskiya matasa a tsarin demokaradiyya sune gishirin tafiya, sau da yawa ‘yan siyasa na amfani da matasa wajen cimma kaiwa zuwa ga wasu madafun iko, ba laifi bane a yi amfani da matasa wajen tallata manufofi a tsarin demokaradiyya, kamar yadda a baya bayannan ya nuna cewa a zaben da ya gabata na Amerika matasa sun taka muhimmiyar rawa wajen samun nasarar shugaban Obama, wannan ta sanya Obaman fashewa da kuka a gaban matasan lokacin da yake yi musu jawabin godiyar sadaukar da kansu da sukayi.

Abinda yake laifi a tsarin siaysar demokaradiyya shine ayi amfani da matasa wajen bangar siyasa domin samun nasara ko ta halin kaka. A mafiya yawancin lokuta ana amfani da matasan ne domin razana abokan hamayya da miyagun makamai, bayan anbasu kwayoyi da wiwi sunsha sun cake. Abinda yafi zama abin mamaki shine su wadannan matasa ‘yan uwanmu suna da masaniyar cewa shi wannan dan siyasa da ya basu kudi suka masa abinda suk yi, ba tasu yake yi ba, sun san da cewar idan fa yaci zabe, basu isa su je wajen da yake ba. Abinda yake zama abin mamaki shine shin matasan nan da suke bari ana amfani da su dan cimma manufar zabe, duk da cewar sun san ‘yan siyasa zasu yi watsi da su da zarar sun ci nasarar samun zabe, sun san ciwon kansu kuwa?  Suna da masaniyar cewa wadannan ‘yan siyasa basu damu da su ba illa kawai sun maida su wata matattakala ta kaiwa zuwa ga samun nasarar zabe? Amsar da muke san mu sani it ace yaushe ne matasanmu zasu ki yarda ana amfani da su a matsayin ‘yan bangar siyasa a bisa kudi kalilan?

Yasir Ramadan Gwale
yasirramadangwale@gmail.com
http://yasirramadangwale.blogspot.com

No comments:

Post a Comment