Tuesday, November 20, 2012

ANKASHE MALAMI, ANKASHE SOJA, ANKASHE DANSIYASA




ANKASHE MALAMI, ANKASHE SOJA, ANKASHE DANSIYASA

Sheikh Jafar Adam yana Sallah a Masallaci, yana karanta al-qur'ani aka bishi har cikin masallaci aka kashe shi (wajen Ibada), har yanzu babu wani abu da aka yi, walau angano wadan da suka kashe an hukuntasu, walau anbiya Iyalansa diyyar jinisa, babu ko daya da ya faru.

Madu Fannami Gubio Dan takarar Gwamna ne a Borno, ranar Juma'a yana dawowa daga Sallar Juma'a aka kasheshi, har ya zuwa yanzu sai dai labari, babu wani mataki da aka dauka, dan sake aukuwar hakan a gaba.

Gen. Mamman Shuwa Soja ne, wanda ya yi yaki domin tabbatar da Najeriya bata balle ba. Amma wasu suka shiga har cikin gidansa suka kasheshi, har yanzu ko ta'aziya gwamnati bata yiwa Iyalansa ba, WAI wannan wanda ya karar da rayuwarsa ta samartaka gaba daya dan bautawa Najeriya kenan.

Hon Abubakar Abba Garko dan majalisa ne a kano, anbishi har inda yake zama ankashe shi. Wannan fa sune Masu yin doka dan al'umma. Wanda shima babu wani abu da za'ayi, haka nan abin zai wuce.

Ankashe Malami, Ankashe soja, Ankashe Dansiyasa Talaka kuwa wannan ko labarin kisansa baka gani a jarida ballantana ka sani, sai dai kaji kudin goro ankashe mutane kaza... Yanzu wa ya yi Saura kenan? Kamar Yadda muke karantawa ankashe wane To Wallahi haka wata rana za'a wayi gari ace ankashini ko ankashe ka, kuma babu wani mataki da za'a dauka. 

Dan haka duk wanda ya dauka Gwamnati zata bashi kariya to yana batawa kansa lokaci ne. Wallahi kodai mu tashi domin kawo karshen wannan zaman zullumi da tsadar rayuwa ko kuma muna ji muna gani kaskanci da wulakanci suyi ta faruwa akanmu, babu kuma yadda muka iya. A garinku kana kallo sojojin JTF zasu zo su kashe wanda suka ga dama su tafi kuma sun kashe . . . (banza anan Duniya) ALLAH ya sawwake! Wadanda aka kashe ba tare da hakkinsu ba, ALLAH shaheed ne, zai yiwa kowa sakayya. ALLAH ka gafartawa wadan da suka mutu da Imani.

No comments:

Post a Comment