Saturday, June 16, 2012

Me Ya Sa Maza Ke Shakkar Likitocin Al'aura???


Me Ya Sa Maza Ke Shakkar Likitocin Al'aura???

Dukkan dangin yabo da godiya da kirari sun tabbata ga Allah ubangijin talikai, tsira da amincinSa su kara tabbata ga fiyayyen halitta annabi Muhammadu da alayansa da Sahabbansa da kuma wadan da suka bi tafarkinsu har ya zuwa ranar saka mako. Ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya bisa cancanta sai Allah, kuma, annabi Muhammadu bawanSa ne, kuma manzonSa ne. Dukkan wanda Allah ya shiryar shi ne hakikanin shiryayye, haka kuma, dukkan wanda Allah ya batar babu mai iya shiryar da shi.
Ya dan uwa mai karatu ina fatan gabanka bazai fadi ba da jin wannan kanu. Kamar yadda yake acikin al'adar musamman Hausa-Fulani ba kasafai ka ke jin maza na tattunawa akan batun da ya shafi al'aurar dayansu ba, shakka babu, wannan sabon abu ne ga 'yan uwana maza aji mutane suna irin wannan tattaunawa, amma ga mata wannan ba wani bakon abu bane kaji mata sun hadu ijunansu suna tattaunawa akan abin da ya shafi matanci ko al'aurar 'yar uwarsu ba tare da nuna wata damuwa ko kunya ba, ta irin haka ne kuma suke samarwa kawunansu da mafitar abin da yake damunsu, domin idan wata ta fadi matsalarta, sai wata ta ce ni da na fada wannan matsalar ga yadda na yi da ita, ga kuma hanyar da na sami mafita, mace ta sami mafita cikin ruwansanyi, ina fatan mai karatu yana biye da ni, wannan ya yi dai-dai da maganar nan da mata ke cewa ciwon 'ya mace na 'ya mace ne.
Hakika, da yawan maza suna shakkar likitocin al'aura. Zaka sha mamaki tare da yin dariya sosai idan kaje asibiti, musamman kaga yadda maza ke shakkar duba al'aurarsu idan bukatar hakan ta kama, idan mace taje asibiti likata ya ce matsalarta tana bukatar sai anduba matancinta, zaka ga bata cika nuna damuwa ba, ba tare da wata tirjiya ba zaka ji mace ta bayar da hadin kai, amma kuma ga d'a namiji  wannan babbar Magana ce, domin duk wani namiji musamman Bahaushe babu abin da ya tsana kamar ace za'a duba al'aurarsa idan bukatar hakan ta kama, kaga mutum yana ta kauce-kauce da kokarin baiwa likita dabaru, wani lokacinma har da kokarin koyawa lokitocin aiki.
Al'aura wani muhimmin sashi ne a jikin dukkan halitta. Ina fatan mai karatu zai gafarceni, shakka babu, al'aura ba waje ne da ya kamata ayi sakaci da shi ba, duba da yadda yake da muhimmanci a rayuwar kowane irin mutum yaro ne ko babba, harma da dabbobi. Mutane da yawa, suna samun matsala a wannan muhimmin waje amma saboda abin da muka fada a baya sai suyi ta boyewa, sau da yawa, idan kaga andubawa namiji al'aurarsa to babu makawa, ya yi dukkan irin zille-zillen da zai yi ya gama,ko kuma ciwo yana cinsa babu yadda zai yi, to nan ne babu yadda ya iya, wannan ce ta sanya da yawan mazaje ke yawo da cututtuka ajikinsu, kaga mutum yana yawo da abu kamar kwallo (ball) a cikin wando,  wannan wata larurace da ta ke damun wasu mazajen, domin, wannan ciwo yana farawa tun daga dan karami ta yadda mutum zai ga warin marenansa na kara girma, amma wasu sun gwammace suyi shiru da bakinsu, har sai abin yakai makura wannan ciwo dai shi aka fi sani da "gwaiwa" ciwo ne da ana iya bayar da magani tun yana karami kamar yadda likitoci suka fada, to amma idan ya yi girma babu yadda aka iya dole a yanke wannan cuta, kaga kenan, ya dan uwana mai karatu wannan kunya bata yi amfani ba anan domin bazai yiwu ba kabar larura tana damunka, kuma kana da yadda zakayi akan wannan  larura, yana da kyau duk lokacin da aka fahimci wani canji a wannan muhimmin waje a garzaya wajen likita domin samun shawarwari da kuma mafita.
Haka kuma, sau da yawa ma'aurata suna fadawa cikin wani mawuyacin hali akan abinda ya shafi al'aurarsu amma sai su kama bakinsu, wasu da yawa sun gwammace su sami mai maganin gargajiya tunda yake shi ba fida yake ba, sai abin ya baka mamaki kaga mutum magidanci yana da larura irin wannan amma sai ya garzaya wajen me magani a hada masa hade-hade, duk kuwa da yana da masaniyar cewa mutumin nan ba karatu ya yi ba. Sannan suma irin wadan nan masu magunguna da suke basu sunaye daban daban, wasu su ce na gyaran aure ko firgita iyali da dai sauransu. Akwai magidantan da suna fama da larurar kankancewar mazakuta amma kuma sun yiwa abin shakulatun bangaro, ta kin zuwa wajen likita ya duba su, shakka babu wannan babbar matsalace da ta ke haddasa kasa sauke nauyin iyali, lallai yana da muhimmanci ga duk wanda yake da wannan larurar ya garzaya wajen likita tun abun baiyi nisa ba.
Wasu kuma, zaka samu irin kumburin da mazakutarsu ta ke da shi ya ragu ainun, amma suma sunyi shiru sunki Magana. Irin wannan matsala babbar matsala ce, domin duk lokacin da aka ce namiji ya kasa sauke nauyinsa a wajen iyalinsa an samu wawakeken gibi, wanda wannan gibi yana iya haifar da komai, hakika, sanin kowane ma'auraci ne cewar mata babu abin da suka fiso irin gamsuwa a yayin da ake tarayya kamar yadda masana suke cewa, irin wannan matsalar ce kan sanya wasu matan marasa tsoron Allah su keta alfarmar mazajensu na aure, ta hanyar fita domin cin amanar mazajen nasu, wannan yana faruwa ne da gagarumar gudunmawa da su mazajen suke bayarwa, ta hanyar kin daukar wani kwakwkwaran mataki tun lokacin da abun yake farko, lallai, ya dan uwana wannan matsala ce da bai kamata aji kunya akanta ba.
Da yawa wasu mazajen suna ha'intar matayensu a yayin ibadar aure. Sau da yawa wasu mazan basu cika lura da cewa su tsaya su biyawa matansu bukatarsu ba, kawai abin da ya dameshi shi ne ya biya tasa bukatar, shakka babu ya dan uwa matarka tana da hakki akanka, hakki na ibadar aure, kamar yadda wasu matan ke korafi, wasu mazan, a yayin ibadar aure, suna kulawa ne kawai da kansu, ba kuma tare da gabatar da wata mukaddima da zata kasance dan sako ga sha'awar matanba, kamar yadda wata ta fada cewa wallahi mijinta kamar yadda dabba ta ke yi haka yake yi, domin da yazo kawai gyara-gyara nan-da-nan ya biya bukatarsa, idan ta koma masa yace shi yagaji, wannan babbar kasawace ga mazaje, idan har iyalinka bata samun gamsuwa tare da kai to shakka babu lamari ya lalace, lallai yana da kyau mazaje su ringa tattaunawa da iyalansu domin tabbatar da cewa basu shiga hakkinsu ba akan wannan ibada.
Bincike ya nuna da yawan mazaje musamman wadan da sukayi haihuwa sama da daya, basa iya yin ibadar aure sai da taimakon magani. Shakka babu wannan babbar matsala ce, ta yadda namiji bashi da kuzarin da zai iya biyawa kansa bukatar larura ta sha'awa sai da taimakon magani, lokitoci sun fada, mafiya yawan wadan nan magunguna suna da illa mai yawan gaske ga lafiyar ita kanta mazakuta da kuma kuzarin namiji. Wani abin mamaki da mallam Bahaushe ya baiwa harkar ibadar aure mihimmanci sosai amma kuma yana yi mata rikon sakainar kashi, zaka sha mamaki idan ka shiga ma'aikatun gwamnati da kasuwanni da makarantu kai da dukkan wajen taron jama'a, kaga yadda ake kaiwa mutane irin wadan nan magunguna, sai kayi mamaki mutum ko sunansa bazai iya rubutawa ba, amma zai baka magani ya yi ta kafamaka ka'idoji kana dauka duk kuwa da digirorin da kake da su, idan ka shiga kasuwanni ko ka duba kan tituna kaga yadda mutane suke yawo da motoci da manya manyan lasifikoki suna yin batsa abin sai ya baka kunya, kaga mutane babu kunya sun taresu suna karbar magani; wallahi, wata rana da naga irin yadda mai sai da irin wannan magani yake yin batsa kiri-kiri a bainar jama'a har sai da naji kunya, kuma ka rasa wanda zai je ya yi masa nasiha, domin su irin wadan nan kalamai ba ko ina ake furtasu ba, don Allah ya zakaji a lokacin da ka ke tare da iyalanka irin wadan nan mutane suna yin muna nan kalamai na basta? Shakka babu abin kunya ne marar misaltuwa, wannan takan sanya kaji karamin yaro yana furta maganganu na ban mamaki.
Akwai cibiyoyi a asibitoci da mutum ya kamata ya je ya shigar da irin wannan korafi nasa na bukatar sha'awa, misali akwai, Heart-to-Heart Centre zaka je ka fadi damuwarka, zasu baka shawarwari masu inganci tare dabaka mafita akan matsalarka, lallai ya dan uwa irin wadan nan masu magunguna ba karya bane maganinsu yana aiki, amma kuma yana da illa, duk da cewa shima maganin na turawa yana da nasa illar, amma ta hanyar zuwa wajen likita shi ne za'a baka shawara, musamman irin abinda ya kamata mutum ya ringa ci da sha kafin ibadar aure.
Lallai bai kamata mazaje su yi shakkar likitocin al'auraba. Shakka babu wannan muhimmin abu ya kamata mu bashi kulawa ta musamman wajen kula tare da duba da kuma uwa uba kariya ta lafiya, da kuma, biyawa iyali bukatunsu cikin kwanciyar hankali, a tashi dan kallo lafiya mai wasa lafiya. Allah ya sa mu dace.
Yasir Ramadan Gwale
yasirramadangwale@gmail.com
http://yasirramadangwale.blogspot.com

No comments:

Post a Comment