Friday, June 22, 2012

AREWA: Kowa Ya Kwana Lafiya Shi Ya So!!!


AREWA: Kowa Ya Kwana Lafiya Shi Ya So!!!
Sa nin kowa ne cewa zama lafiya ya fi zama dan sarki inji masu iya Magana, ni kuma nace yafi zama sarkinma. Kamar yadda dukkanmu muka sa ni ne cewa yanzu kusan Arewa ta shiga wani irin mawuyacin lokaci da bata taba samun kamta a ciki ba a lokutan da suka gabata, kusan a kullum safiyar Allah babu wasu rahotanni da ake karya kumallo da su daga Arewa face harbe-harben bindigogi da tashin Bama Bamai da kisan mummuke da kuma harbin kanmai uwa da wabi da jami'an tsaro karkashin rundunar JTF suke yi a kusan galibin jihohin Arewa, a kullum safiyar Allah.
Hakika wannan tashin hankali ba karamin durkusar da yankin Arewa ya yi ba  ta fannin zaman lafiya, kasuwanci da tattaln arziki. Tun bayan harin boma bomai na ranar 20 ga Janairun wannan shekara ta 2012 da aka kai cikin birnin kano ya dagula al'amuran kasuwanci a wannan birni da ke da tsohon tarihin saye da sayarwa a Yammaci da Arewacin Afurka, kamar yadda muka sa ni kusan gabaki dayan kan iyakokin Najeriya da ke yankin Arewa sun cigaba da kasancewa garkame bayan da gwamnati tayi zargin cewa ana shigo da makamai ta wadannan iyakoki da suka hada da Jimhuriyyar Nijar da Chadi da kuma Kamaru, dubunnan 'yan kasuwa ne suke ratso wadan nan iyakoki domin harkar tijara a Najeriya musamman yankin Arewa, amma yanzu sun durkushe saboda wannan dalili na tsaro da tashin bam da ya addabi Arewa.
Shakka babu, wannan hali na rashin tabbas da kuma tashin boma bomai ya wuce dukkan lissafinmu, domin irin yadda ake kai hare-hare babu kakkautawa ya firgitar da kuma razanar da duk wani mutumin Arewa danta ne ko mazauninta, kasancewar babu wanda yake da masaniyar inda wadan nan miyagu azzalumai zasu kai wadan nan hara-hare na su a kowace rana.
kamar yadda abin ya samo asali, inda muke jin ana kaiwa jami'an tsaro wadannan hare-hare tare da halaka su da jikkata wadan da suke da sauran kwanaki. Yanzu kusan zamu iya cewa abin ya sauya salo, domin daga hare-haren da ake kaiwa jami'an tsaro ankoma hari kan majami'u wato wajen ibadar kiristoci, kusan duk karshen mako sai mun wayi gari da harin kunar bakin wake da ake kaiwa irin wadan can guraren ibada na kirista, tare da hasarar rayukan wadan da basu jiba basu gani ba.
Su wadan nan, wadan da suke kai irin wannan mugun harin, har yanzu kamar yadda hukumomi suke cewa ba'a san ko su waye ba, shakka babu abin zai zama me daure kai da kuma ban mamaki ace duk da irin kwarewa ta jami'an tsaronmu da iya bankado mai laifi amma ankasa sanin su waye hakikanin wadan da suke kai irin wadan nan hare-hare babu kakkautawa, sai dai kawai wata kungiya da ke ikirarin kai wadannan hare-haren ta hanyar amfani da yanar gizo ko intanet suce su ne ke da alhakin kai hari waje kaza da kaza, wanda a zahirin gaskiya babu wata kwakwkwarar shaida da zata nuna maka cewa su ne suke kai irin wadan nan hare hare. Kuma babu yadda Magana a internet zata iya zama hujja domin kowa na iya amfani da internet yana cikin dakinsa ya yi dukkan abinda ya ke so, don haka babu yadda zamu yarda da maganar cewa wasu sun watsa a internet cewa sune suke da alhakin kai gari waje kaza da kaza.
Domin ta ya akayi suke fakar idon jami'an tsaro duk kuwa da suna nan a jibge akan manya da kananan hanyoyinmu, lallai wannan babban abin tuhuma ne ga jami'an tsaro, wani abu da yake bawa mutane mamaki shi ne irin yadda gwamnati ta ke yin karyar cewa suna nan suna aiki tukuru wajen samar da kwanciyar hankali, shin wane irin aiki akeyi wanda har yanzu zaman zullumi karuwa yake mai makon raguwa? ko kuwa irin aikin baban giwa ake yi ta hanyar tufka ta re da warwara, kuma abinda da yake faruwa yau da kullum ya tabbatarwa da al'ummar Najeriya cewa babu wani abu da gwamnati ta ke yi   na kawo karshen wannan tashin hankali, illama amfani da wannan damar wajen dibga mahaukaciyar sata da yashe asusun gwamnati da sunan aikin tsaro.
Sau da dama, jami'an tsaron Najeriya kan kafa hujja da cewar su basu saba da irin wadan nan hare-hare na sari ka noke ba ko harin ta'addanci, anan sai mu ce duk jami'in tsaron da ya yi wannan Magana ya tabbatarwa da duniya cewa lallai basu san aikinsu ba, domin a har kullum shi mai laifi yana amfani ne da hanyar da zai kaucewa fadawa hannun jami'an tsaro, don haka yaushe jami'an tsaro zasu zauna su shanta ke a cikin ofisoshi suna hira suyi zaton masu aikata laifi zasu yi amfani da dabarun da jama'an tsaro suka sa ni, lallai wannan babbar kasawa ce jami'an tsaro suce wai yadda ake kai wadan nan hare haren ya saba da tunaninsu ko masaniyarsu, idan har wanda ba jami'in tsaro ba zai yi amfani da tunani da kwarewarsa wajen shirya shegantaka kuma yaci nasara, ina amfanin jami'in tsaron da ya koyi dabaru kala-kala akan abin da ya shafi harkar tsaro da kama tare da gurfanar da mai laifi.
Kamar yadda ya faru, ankai hare hare akan coci coci a jihohin Plateau da Kaduna da Maiduguri da Bauchi da Neja da sauransu. Abin ya fara kazanta ne bayan da kiristoci suka fara daukar fansa akan musulmi a Jos, inda suke kashe mutanen ba babu ruwansu kuma suke kona dukiyarsu, dukkuwa da bayanan da suke nuna cewa galibi wadan da ake kamawa da kokarin dasawa ko tayar da bom kiristoti ake kamawa da wannan laifi ko yunkuri a galibin inda akaci nasarar kamasu, domin rahotanni sun tabbatar da cewar wanda ya kai harin Cocin Church a Jos da Miyabarkate a Bauchi duk kiristocine, haka kuma ankama kiristocin da suke yunkurin tayar da bom a coci a Bauchi mutum bakwai, banda faston da aka taba kamawa da tarin makamai a Jos da kuma wata mata mai suna Lucy Danga kirista da ta ke safarar makamai zuwa kasarnan, sai gashi baya bayan nan ankama jami'in kwastam da samarwa da kabilarsa ta Berom da miyagun makamai, kuma abin haushi gwamnatin Jos ta fito tana kokarin kareshi, dukkansu babu wani musulmi da aka taba kamawa, amma kuma abin haushi da wadan nan tsagerun kiristoci sai su huce haushi akan Musulmi. Lallai rashin adalcin da hukumomi suke yi ya sake rura wutar wannan lamari, don haryanzu bamuji hukuncin da aka yankewa wadan da muka zayyana ba.
Ya kamata kiristocin Arewa su fahimta, sune mutanan da suka fi kowa cin albarkacin zaman lafiya a Arewa. Shakka babu wannan maganar haka ta ke, cewa kiristocin Arewa sune suka fi amfana da zaman lafiya tsakanin musulmi da kirista, domin galibinsu talakawa ne, don haka irin sana'o'in da suke yi musamman a cikin garin Kaduna zaka samu musulmi ne suke saye, misali masu soya kosai da doya a gefen titi da masu gasa masara da masu tallar ruwan leda na pure water da masu tallar burodi a kan danja da tashoshin mota da masu gidan abinci da masu kananan kantuna zaka samu duk Hausawa Musulmi sune kasuwarsu, da su suka dogara wajen samun dari da kwabo, kaga kuwa da suna da hange da tunani, da su zasu fi kowa son azauna lafiya da juna.
Wani abin mamaki shi ne, Shugaban kasa Kirista, Shugaban sojojin Najeriya kirista, me baiwa shugaban kasa shawara ta fuskar tsaro kirista, babban daraktan 'yan sandan farin kaya na kasa SSS kirista, shugaban majalisar dattawa kirista, gwamnan Kaduna kirista, gwamnan Plateau kirista amma duk da haka sun gaza samar da tsaro ga guraren ibadar 'yan uwansu kirista, to inaga mu musulmi da muke addini daban da nasu? Don haka muna zargin dukkan wadan can bangarori da kitsa wutar wannan tashin hankali domin cimma wata boyayyar manufa da suke da ita, wanda ya zuwa yanzu ta bayyana cewa Gwamnatin Jos tana da hannu a galibin rikice-rikicen da ke faruwa a jihar.
Kuma tun daga fadar paparoma dake Vatican da kungiyar CAN dake Najeriya, babu wanda ya yi kira da a hukunta kiristocin da ake kamawa da yunkurin tayar da boma bomai ko dasa su, ko kuma masu safarar makamai; haka kuma, ankaiwa Musulmi hari ranar sallar a Jos babu wani kirista da ya ke da fada a ji a kungiyar CAN da ya fito ya bukaci lallai ayi bincike don gano wadan da suka kaiwa musulmi hari domin a hukuntasu, haka kuma, irin kisan kiyashin da akayiwa musulmi ana zubawa a rijiya da shadda a zankwa a lokacin rikicin bayan zabe babu wani kirista tundaga fadar paparoma da ya zargi kiristoci da aikata ba dai-dai ba. Amma wai har shuagab CAN Oritsejafor yake cewa wai musulmi basu fito sunyi allawadai dinda ta kamata ba da harin da aka kai a Madalla ta jihar Neja ba.
Amma tunda yake suna ganin wannan hanyar da suka biyo suna ganin itace mafita, muna tabbatar musu duk da musulmi suna cewa a zauna lafiya, su sa ni wallahi mu ba matsorata bane, kuma daga yanzu duk wanda ya kwana lafiya shi ya ga dama, kuma munce CAS ga duk wanda ya ce mana kule, mu daura zare da su, muga su wa zasu kasa, tunda yake jami'an tsaro sun gaza samar da tsaro a tsakanin 'yan Najeriya mu Musulmi wallahi zamu iya baiwa kanmu tsaron rayukanmu da dukiyoyinmu da taimakon Allah da kuma kwazon da muke da shi, kamar yadda duk  muka sani ankaddamar da aiki da shari'ah a Arewa kuma akwai 'yan Hizba a jihohinmu, dukkanmu mazanmu da matanmu sai mu zama 'yan Hisba domin baiwa garuruwanmu aminci.
Kuma wallahi kiristocin Arewa su sa ni, ta re matafiya musulmi da suke yi a kauyen gwanin gora akan hanyar Kaduna zuwa Abuja, wannan su zata kwabewa, domin kauyen nawa yake, daga yanzu sai mu ringa tahowa cikin ayari duk karshen mako daga Abuja zuwa Kaduna zuwa da komawa, kuma kowa ya yi guzurin gora don kare kansa, muga idan da akwai dan iskan da ya isa ya tare mana hanya, kamar yadda yake a dokar kasa kare kai ba laifi bane, to wallahi zamu yi dukkan mai yuwuwa wajen muga mun kare kanmu har Allah ya maidamu gidajenmu Lafiya.
Idan kuwa sun zabi zaman lafiya, su sa ni wallahi mu Musulmi munfi kowa kaunar ganin a zauna lafiya, domin munyi imani da Allah da Manzon Allah kuma munyi imani da littafin Allah al-qur'ani, Allah baice ka kashe mutum don ba addininku daya ba, don haka duk wannan abin da yake faruwa al-qurani ya riga ya bamu mafita. Don haka wanda yake fatan a zauna lafiya muna maraba domin mu musulmi ba masu son tashin hankali bane, duk kuma wanda yake tunanin mu matsorata ne to ya tabbatarwa da kansa cewa ya yi kuskure a shirye muke mu fuskanci duk wani dan iska mara kaunar zaman lafiya.
Yasir Ramadan Gwale
yasirramadangwale@yahoo.com
http://yasirramadangwale.blogspot.com

1 comment: