Friday, June 22, 2012

Al-Majirai Ma 'Ya 'Ya Ne Suna Da hakkin Samun Ilimin Boko amma . . .!




Al-Majirai Ma 'Ya 'Ya Ne Suna Da Hakkin Samun Ilimin Boko amma…!
Rahotannin sun tabbar ta da cewa akwai kusan al-majirai sama da miliyan 9 a Najeriya mai mutane kimanin sama da miliyan 165, wanda wannan yake nuna al-majirai sun kai kusan kashi 1.06 a Najeriya, kimanin yawan mutanan jihar Delta da Bayelsa. Lallai wannan adadi babbar barazana ce ga tsaro da zaman lafiyar wannan kasa, kuma alamu sun nuna cewa wannan adadi yana karuwa cikin sauri. Kusan idan baka ce duka ba, to sama da kashi 8 cikin goma na wannan adadi sun fito ne daga jihohin Arewa, wanda masana ke cewa talauci yana da yawa a kusan jihohin Arewa maso gabas da kuma Arewa maso yamma, lallai wannan babban kalubale ne ga gwamnatocin wadan nan jihohi da kuma masu hannu da shuni domin ganin antashi tsaye haikan wajen yakar fatara da bakin talauci da suka mamaye wannan yanki.
Kamar yadda muka sani a yanzu kusan dalilin da yake sababba al-majiranci shi ne mawuyacin hali da galibin mutanan kauyuka ke ciki na rashin iya daukar dawainiyar iyalansu, dan haka ne wasu suke yanke shawarar turasu karatun allo inda rayuwa ta ke da dama-dama, inda galibi yanzu zaka samu almajirai suna watangaririya a kusan manyan birane, domin neman abinda zasu ci, wasu kuma suna ragaita babu karatun sai neman dari da kwabo.
A can baya ana tura yara zuwa gabas ne kamar yadda ake cewa domin neman karatun al-kurani, inda kusan duk bayan kammala noma da girbe amfanin gona ake tura yara zuwa musamman kasar Barno, domin haddar al-kurani mai tsarki, alhamdulillahi a wancan lokaci birnin Maiduguri ya ya ye dalibai da daman gaske wadan da suka hardace alkurani mai girma hadda ba ta wasa ba, wannan ta sanya birnin ya shahara da mahaddata al-kurani har ya zuwa yanzu, amma kuma zance na gaskiya yanzu abin ba haka yake ba, domin galibi yaran da ake turawa da suke da kananan shekaru daga zarar sunyi wayo sun bude ido sai su watsar da karatun al-kurani su koma aikin neman abin batarwa agun 'yan daudu masu dafe-dafe ko kuma kaji yaro yabi makida 'yan koroso ya zama yaronsu, kaga kenan wannan ita ce cikakkiyar lalacewa domin yaron da yazo neman karatun al-kurani ya bige da bin 'yan daudau ai lamari ya baci, kuma lissafi ya rushe.
Ada can yadda muka sani, al-majirai suna da wasu 'yan sana'o'I da suke yi. Da yawan al-majiran wancan lokacin da wuya ka gansu yara kanana, kamar na yanzu, zaka samu suna yin sana'ar wanki da guga ko wanki tare da d'amin hula, ko kuma sana'ar wankin takalmi da dinkinsa (shushana), ko kuma sana'ar likin robobin da suka fashe ko suka tsage, galibi wadan nan sune mafiya yawan sana'o'in da almajirai suke yi a wancan lokacin sabanin na yanzu, da yaran kusan suka koma rabi suna bara rabi kuma suna sata, wato yaki halal yaki haram, watakila wannan ya faru ne bisa yadda kudade suke da yawa a hannun mutane, da kuma, yadda abun bukatuwar yau da kullum yake kara yawa.
Kamar yadda muka sani ne, a 'yan watannin baya da suka gabata shugaban kasa ya bude katafariyar makarantar boko da kuma allo ta zamani a jihar sokoto. Bude wannan makaranta yazo ne bayan shugaban kasa ya yi wannan alkawari a lokacin da yake yakin neman zabe cewa idan yaci nasarar zai gina irin wadan nan makarantu guda 121 a fadin Arewacin Najeriya, a cewarsu kuma anware kudade kusan Naira Biliyan dari hudu (400 Billion) domin wannan aiki. A daidai wannan gabar abubuwa da yawo zasu iya tasowa, kamar yadda dukkan ninmu muka sani Najeriya kasa ce mai yawan kabilu da mabanbantan al'adu da kuma addinin musulunci da na kirista, anya kuwa kiristocin Najeriya zasu iya shiru ko su zura ido suna kallon Shugaban kasa yana narkar da irin wadan nan makudan kudade da sunan gina makarantar Allo a Arewa? Domin kamar yadda yake a bayyane yake cewa, kiristocin Najeriya sun zama kamar kishiya ga musulmin Najeriya, domin duk sadda gwamnati ta yi wani abu da ya dadadawa musulmi suma sai sunyi korafi ko kuma kirkiro wani abu da suma za'a rika basu kudade, misali, kowa yasan gwamnati tana ware makudan kudade domin hidimar aikin Hajji da musulmi suke yi a kasar saudiyya a dukkan karshen shekarar Musulunci wato a watan zul-Hajji, irin yadda gwamnati take kashewa mahajjata kudi a kasa mai tsarki ya tsonewa kiristocin Najeriya ido ainun, domin idan zamu iya tunawa Solomon Lar a lokacin da yake Gwamna a Jihar Plateau ya yi ta korafi ga gwamnatin shagari cewa da taje tana kashewa musulmi kudi suna hawan duwatsu a kasar Saudiyya me zai hana su zo Jos su ringa hawan duwatsu, ya dauka cewar kawai duwatsu ake hawa a can, wannan ta sanya kiristoci suka kasa hakuri da jurewa inda suka kirkiro wani abu wai shi aikin Hajjin kirista wanda kowa yasan babu shi a addinin kirista.
Wannan ta sanya suma yanzu gwamnati take ware makudan kudade domin wadan da zasu tafi aikin Ibada Jerusalem a kasar Israela, ba komai ya sanya suka yi wannan ba illa kawai nunkufurci da bakin cikin yadda gwamnati take yiwa musulmi hidima, amma kuma duk da haka aikin ibadar nasu yaki yin kasuwa domin da wahala kaji talakawansu suna zuwa wannan ibadar galibi sai masu hannu da shuni wanda suma suna zuwa ne kawai bude ido da yawan shakatawa, domin ibadar batada wasu rukunai da wasu muhimman al'amura da ake gabatarwa a yayin ibadar; sun manta cewa aikin Hajji da musulmi suke zuwa kasar Saudiyya rukuni ne daga cikin rukunan musulunci.
Wannan ta sanya dole mu kalli wannan gina makarantu ta wannan fuska, domin idan har ba wata makarkashiya bace ko kuma wata manakisa a cikin shirin ba, to babu yadda za'ayi kiristocin kasarnan su tsaya suna kallon gwamnati tana kashe wadan nan makudan kudade ba tare da suma sun kirkiro nasu makarantun allonba, sannan idan muka tsaya tsayin daka muka yiwa wannan lamari kallo na tsanaki da kuma cire son zuciya zamu tarar akwai illa da yawa acikin wannan shiri, domin me ya sanya aka baiwa makarantar sunan ta al-majirai kawai? idan da gaske gwamnati ta ke yi me ya sanaya bazata ce al-majiran suje makarantar boko ta gwamnati kamar yadda 'ya 'yan kowa suke zuwa ba? Me ya sanya aka ware makarantar kawai sai al-majirai? Shin al-majirai sunfi kima a wajen gwamnati ne? ko kuma sunfi zama barazana gareta shi ya sanya ta killace su yasu yasu?
Kamar kuma yadda aka ce, tsarin karantarwar zai yi dai-dai da na makarantun boko, wato yara su sanya kayan makaranta (Uniform) da litattafai da azujuwa da kuma tebur da yara suke zaune, duk wannan ya nuna shirin ba da gaske akeyinsa ba, domin me yasa za'a ce yara sai sun sanya kayan makaranta? Ba bu wanda ke kin tsafta, amma a irin yadda muka taso a can baya bamu tarar ana zuwa makarantar allo da Uniform ba, don a fakaice wannan ana nunawa yara kyamar wancan tsari na karatun allo da ake yi da malami a zaune a kasa, kuma shi kansa zama akan tebur wannan ma wata matsala ce, domin ya ci karo da tsarin tarbiyyar da aka taso da karatun allo a kasar Hausa, ba laifi bane a shigo da sabbin tsare-tsare a dukkan harkar ilimi, amma yana da kyau a yi la'akari da irin yanayin zamantakewarmu da kuma al'adunmu. Shin su kuma makarantun Islamiyya na zamani da 'ya 'yan kowa da kowa suke zuwa me ce makomarsu?
Sannan a wannan sabon tsari na makarantu, yara zasu shiga aji kamar yadda tsarin makarantun boko yake inda malami zaizo yana koyar da su harshen turanci da lissafai kamar yadda aka tsara da safe sannan kuma da yamma suyi karatun allo tare da alaramma kamar yadda aka saba, nanma akwai illa mai yawan gaske, domin, da alaramman da yake karantar da yara tare da bulala a hannunsa yana zune akan buzu, da kuma malamin da yake karantar da yaran suna zaune akan kujeru yana basu karatu watakila har yana hadamusu da wake-wake irin wadan da akeyi a galibin makarantu, wa ka ke jin wadan nan yara zasu fi kauna? Wane darasi kake zaton yaran zasu fi sha'awa tsakanin karatun allo da kuma na makarantar Boko? Ba muki a koyar da al-majirai karatun boko ba, amma shakka babu game shi da akayi da karatun allo wannan akwai makarkashiya a ciki, domin a hankali za'a zarewa yaran son karatun al-qurani da kin duk wani darasi da yake da alaka da Al-qurani ko addini, kamar yadda a yanzu haka acikin makarantunmu na sakandare zaka samu galibin yaranmu basa son darasin Islamic Studies saboda duk makarantar da ka shiga zaka samu galibi malamin da yake koyar da darasin addini na Islamic shi ne mai horo(displine Master) wanda ga duk mai hankali yasan da gayya acikin wannan shiri, yara sun tsani malamin saboda irin yadda yake dukansu wannan ta basu damar tsanar darasin da yake koyarwa, bayan kuma ankai darasin karshen lokaci ta yadda duk yara sun gaji kowa alla-alla yake a kada karaurawa ya kama gabansa ya tafi, kaga duk wannan mun san akwai manufa a cikinsa.
Don haka wannan sabon shiri na gwamnatin tarayya na game makarantun Allo da na Boko ba shi ne alfanu ga almajirai ba, idan har da gaske gwamnatin ta ke son gyara harkar almajiranci da al-majirai. Idan har da gaske gyaran ake son yi kuma al-majiran ake son taimakawa domin su samu wannan ilimi na zamani, to wajibine gwamnati ta taimakawa da iyayansu ta hanyar yakar cinhanci da rashawa da kuma bijiro da ayyukan da mutane zasu samu aikin yi, da kuma inganta harkar noma ta wannan hanya kowane yaro sai ya koma gaban iyayansa ya yi karatun boko a gabansu, suna bashi kyakykyawar kulawa kamar yadda kowane uba ya ke lura da dansa, domin suma al-majirai 'ya 'ya ne kamar kowa.
Ko kuma, gwamnati ta inganta tsarin da muke da shi na karatun tsangaya ta hanyar zamanantar da tsangayar a gina musu bandakuna da dakunan kwana da famfunan samun ruwa da baiwa alarammomin abinda zasu ringa daukar dawaniyiyar yaran da kuma iyalansu, da kuma shirya musu bita akai-akai, sannan kuma gwamnati ta sanya su, su ringa zuwa makarantun boko na inda suke suna haduwa da sauran yaran al'umma suna karatu tare, duk wannan karkashin kulawar gwamnati da kuma alarammomin, sannan da koyar da su sana'o'in hannu da kuma basu dan abinda zasu juya, wannan ita ce hanyar da gwamnati zata ceci al-majirai amma ba ta hanyar game makarantun allo da na boko ba, Bahaushe ya ce ayi dai mu gani . . .!
Yasir Ramadan Gwale
yasirramadangwale@gmail.com
http://yasirramadangwale.blogspot.com

1 comment: