Friday, February 10, 2012

Siriya: Bashar Al-Assad, Karshen Alewa kasa!

Kusan yanzu idan akwai wani abu da yafi kisan kare dangi a duniya to za’a iya kiran abinda Bashar Al-assad ya ke yi a kasar da yake mulki tsawon lokaci da jam’iyyarsa ta Ba’ath ta shafe shekaru kusan 43 tana yi, musamman kisan kiyashin da ya ke yi a Birnin Homs da Dar’a. Hakika abin da ya ke faruwa a wadan nan birane ya yi muni kwarai da gaske kamar yadda Saleh Al-Dabbakeh da yake aiki karkashin International Human Right Groups a kasar Siriya ya shaidawa gidan talabijin na BBC cewar munin abin da yake faruwa a wannan birni na Homs ya yi yawa ainun.

Haka shima wani matashi Ez-Al-deen Al-halabi daga tsakiyar birnin Homs ya shaidawa gidan talabijin na Al-Jazeera ta wayar tarho cewar hakika mutanan wannan birni suna cikin wani irin mawuyacin hali na harbe-harbe babu kakkautawa daga dakarun da gwamnatin Bashar Assad da ta jibge a wannan birni, da gidan talabijin din na Al-jazeera suka tuntubi Salam el-Homsy ta hanyar amfani da Skpe yace mutanan wannan gari suna fuskantar karancin abinci da ruwan-sha da magunguna ga shi kuma babu wutar lantarki a wannan gari, ya kara da cewar akwai matsananciyar yinwa tsakanin al’ummar sannan kuma yace wani likita ya shaida masa cewa kananan yara da yawa suna mutuwa.

A rahotan da yake aikawa da gidan talabijin na BBC daga birnin Bierut mai makotaka da kasar Siriya Jim Miur ya ce rahotannin da suke fitowa daga wannan birni, yace hakika mutane suna cikin tsanani kamar yadda ya yi hira da wani magidanci da ya fusata yace ina dukkan kungiyoyin kare hakkin bil-Adama suna gani Assad zai karar da al’ummarsa domin ci gaba da mulkinsa na danniya da cin zali.

Ita ma a nata bangaren Majalisar dinkin Duniya ta ce kusan tundaga fara wannan bore ankashe fiye da mutane 5,000 a kasar ta Siriya wanda dakarun gwamnatin Assad sukayi, tace a makon da ya wuce kawai an kashe fiye da mutane 400 a wannan birni na Homs inda ‘yan Adawa suke da karfi, kididdiga dai ta nuna cewa muslumi sunni sune suke da rinjaye a wannan kasa.

Haka kuma, rahotanni suna cewa manyan sojojin kasar suna ballewa daga bangaren gwamnati suna komawa gurin ‘yan adawa kamar yadda wani gidan talabijin mai goyon bayan ‘yan adawar ya ke fada a shirye-shiryensa da yake watsawa da harshen larabci, inda kuma sukace dukkan alkaluman da ake bayarwa akan kisan da dakarun gwamnati sukayi ya ninka ninkim ba ninkim.

Bashar Al-Assad: kusan za’a iya cewa duk abinda ya keyi gadone da mahaifinsa ya barmasa, don shima Hafiz Al-Assad ya aikata irin wannan danyen aikin a shekarun 1980s ya halaka dumbin magoya bayan ‘yan jam’iyyar nan ta Islama wadda ake kira Muslim Britherhood bayan boren da sukayi na Allah wadai da mulkinsa a wancan lokaci. Shi dai Assad yana bin tsarin kama karyar da jam’iyyarsa ta Ba’ath ta ke aiwatarwa kusan tun a shekarun 1963, ita dai wannan jam’iyya wani mutumne da ake kira Micheal Aflaq ya kafa ta kuma tun wannan lokaci har kawo yanzu itace ta ke mulki, kuma banda mulkin danniya da kama karya babu abinda suka sanya a gaba. Shi dai Assad ya fito ne daga wata karamar kabila da ake kira Al-awites marar farain jini tsakanin ‘yan kasar.

A cikin ‘yan kwanakin da suka gabata majalisar Dinkin Duniya, karkashin kwamitin sulhu suka kada kuri’a akan wani kuduri da kasashen yamma irinsu Amerika da Birtaniya da Faransa suka kawo da yake cewa lallai Assad ya yi murabus, amma kasashen Rasha da Chana suka hau kujerar naki akan wannan kuduri inda suka ce wai yakin basasa na iya barkewa a wannan kasa. Kusan duk wannan abin da yake faruwa shi shugaba Bashar Al-assad yana rawa ne da bazar wadan nan kasashe domin yana da masaniyar cewa duk irin wannan babatu da kasashen yamma sukeyi akan kasarsa gara musu shi akan wani sabon shugaban Siriya da zaizo da basu sanshi ba, domin suna tsoron kada su kori Assad kuma su sami wani shuagaba da zai sukurkuta alakar kasar Syria da Israela, domin ko babu komai Assad ya yi shiru akan tuddan Golan da Isreala ta mamaye.

Wannan cema ta sanya ake ganin Shugaba Assad yana yin duk abin da yake yi ba tare da wani tsoro ko shayi ba. Amma duk da kungiyar kasashen larabawa basa tabuka wani abin kuzo mu gani su ne suka fara gabatar da wannan kuduri a gaban kwamitin sulhun majalisar dinkin duniya na fatattar shi Assad, inda Firaministan kasar Qatar Hammad Bin Jassim Althani ya wuce gaba wajen gabatar da wannan kuduri, kuma sukaci nasara Amerika ta goyi bayansu akan lallai Assad ya sanna yi, ita dai wannan kungiya ta kasashen Larabawa daman shi Assad baya kallonta da wata kima ko daraja da zata iya zama barazana a gareshi domin yasan cewa kusan suna zaman ‘yan amshin shatan kasashen yamma ne, domin a ganinsa da suna da tasiri da ya gani akan kasar Iraqi da Libiya da Tunisiya.

Kungiyar ta kasashen Larabawa ta tura wakilai da suke je Birnin Damascus don tattaunawa tsakanin Assad da ‘yan Adawa, da kuma ziyartar inda tashin hankalin ya yi tsamari kamar birnin Homs domin suga yadda za’a iya sasantawa tsakanin gwamnatin Assad da ‘yan Adawa karkashin Muslim Brotherhood, inda suka je suka dawo ba tare da samun wani mataki na kuzo mu gani ba. Haka shima sarki Abdallah na kasar Saudiyya yaga baiken kasashen Rasha da Chana bisa matakin da suka dauka na hawa kujerar naki akan Siriya inda ya zargesu da abin kunya, yace bai kamata a tsaya a zura ido ga Assada yana cigaba da kisan talakawa bayain Allah ba.

Idan zamu iya tunawa wannan juyin juya hali ya samo asali ne daga kasar Tunisiya inda wani mutum mai saida kayan marmari da ake kira Bouzizi ya bankawa kansa wuta a gaban ginin majalisar dokokin kasar sakamakon matsananciyar rayuwa da yace yana fuskanta, wannan ta haifar da zanga-zanagar da tayi sanadiyar awon gaba da shugaba Zainul Abedeen Ben Ali, inda daga nan ta harbu zuwa kasar Masar inda aka jiyo Shugaba Husni Mubarack yana kira ga kasashen yamma cewa muddin suka bari akayi awon gaba da shi to su kwan da sanin cewa dukkan shugaban da zai biyo bayansa mai tsananin kishin addinin Islama ne kamar yadda ya ce, amma wannan barazana bata hana kasashen yamma su juya masa baya ba wajen marawa ra’ayin jama’a baya, babu girma babu arziki Mubarack duk da irin daular da ya shiryawa kansa ya sauka daga kujerar mulki yana ji yana gani ya koma sham el-Sheikh da zama.

Haka abin yake ga shugaba Ghaddafi, inda ya yiwa al’ummarsa barazana akan yin bore, haka ya debo mutane sojojin haya daga kasashen Afirka da ake kira Sub-Saharan Africa suka dinga kashe jama’arsa musamman a biranen Misirata da wasu garuruwa da suka hada harda Benghazi da Bani-walid da wani shashi na Birnin Tripoli babu ji babu gani kawai domin sun juyawa shugabancinsa na shekaru 42 baya, nan yaja kunnen NATO cewa muddin suka kuskura suka sanya baki akan abinda ya shafi Libiya to zai haifar da yakin basasa, kuma idan har suka bari ya kubuce a zaman shugaban Libiya to al-qa’ida ce zata karbi ragamar mulkin kasar Libiya, shi ma dai wannan barazana a banza domin NATO ta shiga inda ta mara baya ga ‘yan adawa kuma suka ci nasarar kifar da azzalumar gwamnatinsa da batasan kimar jinin al’ummarta ba, haka kungiyar ‘yan adawa karkashin jagorancin NTC suka ci nasara.

Shararren malamin nan na Musulunci Sayyid Qutub ya ce neman ‘yanci wata bishiyace da bata tsiro bata tofo har sai masu nemansa sun shayar da wannan bishiya da jinin jikinsu, haka kuwa ya faru domin al’ummar kasar Masar sun kwanda sanin cewar matukar za’a nemi ‘yanci sai anrasa rayukan mutane da dama, duk da barazanar Mubarack haka suka fita dandalin ‘yanci na Tahrir domin rera sananniyar wakar nan ta neman ‘yanci ta al-shab yurid, isqat al-Nazim. Haka shi ma babban MUFTI na kasashe Larabawa Shekh Dr. Yusuf Al-Qardawi ya yi wata fatawa a khudubar juma’a da ya yi daga kasar Qatar inda yace ya halatta duk wani shugaba da ya juya baya yana yakar al’ummarsa a kashe shi idan anganshi, wannan ya yi tasiri kwarai da gaske wajen kawar da shugaba Gaddafi, domin yaci amanar mutanan da ya shafe sama da shekaru 40 yana shugabanta.

Shima a kwanakin baya da yake hira da jaridar Daily Telegraph ta Birtaniya Shugaba Bashar Al-Assad yace matukar kasashen yamma suka bari ‘yan adawa karkashin Muslim Brotherhood sukaci nasarar kifar da gwamnatinsa to kuwa wata mummunar girgizar kasacce zata faru a kasashen Larabawa, lallai duk wanda yaji wadan nan kalamai na Assad yasan cewa ya kidime; domin ya manta da irin kisan kiyashin da mahaifinsa Hafiz Al-assa ya yi alokacin da yake mulki kuma ya manta da dubban mutanan da suka halaka a biranen Aleppo da Constantinople da Jerusalem da Baghadad da Damascus duk wannan bai haifar da girgizar kasa ba sai mulkin wani mutum kwaya daya Assad shi ne zai haifar da girgizar kasa!

Hausawa dai suna cewa abin da yaci Doma baya barin Awe duk, da irin wannan barazana da Mubarack da Gaddafi sukayi bai hana guguwar sauyi tayi awon gaba da su ba, don haka Assad ya kwana da sanin karshen alewa dai kasa haka shima zai bi sahun wadan nan shugabanni, watakila irin kisan da za’ayi masa ya fi na Gaddafi muni, duk da yana ikirarin yana da magoya baya a birnin Damascus, a gefe guda kuma yana tunanin cewa Hezbollah da kasar Iran zasu bashi goyon baya wanda a hakikanin gaskiya duk wanda yake bibiyar siyasar kasashen gabas ta tsakiya yasan da cewa Assad yana yaudarar kansa ne kawai da tunanin samun goyon baya daga Iran da Hezbollah.

Kamar yadda Mutanan Benghazi da Tunis suka shaki iskar ‘yanci muna fatar nan bada jimawa ba ‘yan uwanmu da suke biranen Homs da Dar’a dama wadan da suke a birnin Damascus suma zasu shaki irin wannan iskar, kamar yadda juyin juya halin kasar Faransa ya ce dole a baiwa kowa ‘yanci batare da la’akari da launin fata ko kabila ko addini ba, tunda ‘yancin dan Adam din da kasashen yamma suke ta kwarmato Assad na takawa, amma kuma muna da yakinin cewa duk da irin dasawar da suke yi a yanzu lokaci kankani zasu juya masa baya.

Haka shima Shugaba Ali Abdallah Saleh na Yemen ba’a barshi a baya ba wajen aikata ta’addaci ga a’ummarsa ta hanyar yin amfani da jami’an tsaro suna muzgunawa masu bore da mulkin danniya nasa, wanda a karshe yakeson gadar da dancikinsa. Bayan da yake ta kokarin fararutar ‘yan alka’ida domin ya farantawa Amerika da sauran kasashen yamma, shima muna nan muna jiran lokacin da kasashen yamma zasu juya masa baya kamar yadda hakan ta faru da takwaransa Mubarack inda al’ummarsa sukayi ta rera wakar neman ‘yanci ta al-sh’ab yurid isqat al Nizam da sannu suma mutanan Yaman zasu sami irin wannan ‘yanci.

Yasir Ramadan Gwale

yasirramadangwale@hotmail.com

http://yasirramadangwale.blogspot.com

No comments:

Post a Comment