Tuesday, February 7, 2012

Dr. Rabiu Musa Kwankwaso: Albasa Tayi Halin Ruwa!

Dr. Rabiu Musa Kwankwaso: Albasa Tayi Halin Ruwa!

Kusan akwai wani abin mamaki dangane da sake zaben Muhammad Rabiu Musa Kwankwaso a matsayin gwamnan kano a karo na biyu. Hakika ya zowa da dama da abin mamaki kwarai da gaske cewa kwankwaso shi ne mutumin da kanawa suka sake zaba a 2011, domin sanin kowane mutumin kano ne cewa gwamnan bai kwashe da dadi da al’ummar kano ba a shekarar 2003 lokacin da ya nemi sake komawa a karo na biyu. Kamar yadda muka shaida an rabu dutse hannun riga tsakanin kwankwaso da al’ummar jihar kano, don gwamnan ya so komawa a wani lokaci mai cike da jumurda dangane da al’amuran da suke da alaka da aiwatar da aiki da shari’ar musulunci.

Kamar yadda muka sani ne cewa gwamnan da ya fara kaddamar da aiki da shari’a shi ne tsohon gwamnan jihar zamfara Sanata Ahmad Sani Yariman Bakura a shekarata 2000, wannan ya tsuma al’umma da dama a Arewacin Najeriya musamman al’ummar kano, inda akayi ta shirya laccoci da wa’azi dangane da burin da al’umma suke da shi na aiwatar da aiki da shari’a a kano kamar yadda akayi a zampara, wannan ta sanya gwamnan kano na wannan lokaci kwankwaso ya shiga wata sabuwar tsaka mai wuya dangane da kiran da jama’a suke masa da ya kaddamar da aiwatar da aiki da shari’ar musulunci bayan matsin lamba da ya sha daga kusan kowane bangare na al’ummar kano musamman wadan da suke da ruhi na addini, rahotanni sun nuna cewa a wannan lokacin gwamnan ya kaddamar da shari’ar ne ba don yana so ba, sai don babu yadda zaiyi.

Wannan soyayya ta shari’ar musulunci da al’ummar kano suka nuna ta haifar da samuwar takarar tsohon gwamna Mallam Ibrahim Shekarau, wanda akace ya fuskanci matsananciyar rayuwa a lokacin da yake ma’aikacin gwamnati, a lokacin Rabiu Kwankwaso, don ance yana halartar kusan wa’azozin da akeyi na motsa zukatan jama’a dan gane da shari’ar Musulunci, a saboda yana halartar tarukan da suke da alaka da shari’ar Musuluncin ne hakan ta janyo akace an maidashi malamin makaranta daga sakataren dun-dun, Allah masani.

Bayan da gwamna Mallam Ibarhim Shekaru ya shafe shekaru takwas a kan kujerar gwamnan jihar kano ya mara baya ga takarar Mallam Salihu Sagir Takai kasan cewarsa mai ruhin addini, wannan ta sanya duka bangarorin biyu suka fuskanci bakar adawa daga ‘yan hamayya cewa an dauko masu hannun jarirai dama wasu kalamai marasa dadin ji aka rika alakantasu da Sardaunan da dan takararsa.

Sai dai kuma, kwankwaso ya nuna aniyarsa ta sake zama gwamna a karo na biyu. Bayan ya tsallake turaku da daman gaske da jam’iyyarsa ta sanya masa, Gwamnan wanda ya yi ta amfani da kausasan kalamai a lokacin da yake yakin neman zabe, kalamai masu tsoratarwa kwarai da gaske. Domin a wata maganarsa da kusan ta zama zaurance tsakanin al’ummar kano wacce akajiyoshi yana cewa “Ja janjaros danja” da kuma wata magana da itama ta zama kamar zaurance wacce da yawa daga cikin ‘yan jam’iyyarsa baka rasasu da ita a waya inda yake cewa “wannan Ja shi ne maganin mayu, maganin MAHAHAA” aciki har yake cewa batun zabe anyi angama Rabiu kwankwaso yaci zabe a bashi abinsa” wanda duk wanda yaji wadan nan maganganu yasan ba’a taki zaman lafiya ba.

Tabbas da ace tsohon gwamna Mallam Ibarhim Shekaru yana son fitina a wancan lokaci da ya gurfanar da tsohon gwamnan a bisa wadan nan kalamai da suke barazana ga tsaro. Bayan haka kuma akwai wasu kalamai suma da suke barazana ne ga tsaro da zaman lafiya inda yake cewa “ko asa kaci GORO dan UJULE, ko asa maka JANBAKI, ko kuma yaro kaji WUJU-WUJU kazaga ka rasa ina gabas ta ke”, shakka babu duk wanda yaji wadan nan kalamai yasan barazana ne ga zaman lafiya a dai-dai wannan lokaci da jihar kano take da bukatar kyakkyawar al’kibla, amma da yake tsohon gwamnan ba mai son tashin hankali bane sai bai yi komai akan wadan nan kalamai na Rabiu kwankwaso ba.

Jama’a da dama musamman ma’aikatan gwamnati suna fargabar dawowar tsohon gwamnan a matsayin sabon gwamna domin anjiyoshi a lokacin yakin neman zabe yana cewa duk wani ma’aikaci da gwamantin Mallam Ibrahim Shekarau ta dauka idan ya dawo to sunansa korarre, da kuma ‘yan famsho wadan da suna masa ganin ya hanasu hakkinsu a lokacin da yake gwamna, wadan nan dama wasu da dama sun sanya jama’a tsoron dawowar kwankwaso a matsayin gwamnan kano, domin anringa ganin makamai tsirara a hannun magoya bayansa a dik sanda ya fita yakin neman zabe.

Baya ga haka kuma ana ganin lokacin da kwankwason yake kokarin dawowa lokaci ne da jam’iyyarsa ta PDP ta dage sai anzabi shugaba Jonathan wanda sukayi masa lakabi da MAINASARA JONATHAN, a daya bangaren sauran al’umma kuma suna ganin wannan dama ce ta ‘yan Arewa, wannan ta sanya da yawan mutanan Arewa suke kyamar PDP domin a tsahon lokacin da suka shafe suna mulki a kasarnan sun kasa samarwa da al’umma ingatacciyar wutar lantarki duk da irin biliyoyin da aka kashe malala, da yawan mu ‘yan Arewa muna Allah wadai da manufofin jam’iyyar PDP domin babu abin da suka sanya a gaba face shan jinin ‘yan Najeriya ina nufin matsanan ciyar rayuwa domin tun daga 1999 zuwa yau babu wata matsala da zaka iya cewa yau gashi sun dauka kuma suna kai karshenta, kullum sai karairai iri daban-dabn.

A lokacin da kwankwason yake yakin neman zabe ya yi alkawari ga jama’ar jihar kano da daman gaske, inda a karamar hukumar Kibiya mukaji yana rantsuwa cewa waallahi dukkan alkawuran da ya dauka sai ya cika su, muna nan muna jira kuma muna fatar su zama hujja a gareshi ba hujja akansa ba. Bayan ya dare kan kujerar gwamna, kwankwason ya fara ne da kididdigar ma’aikatan gwamnatin domin fitar da ma’aikatan jabu kamar yadda suka yi ikirari cewa suna nan da yawa suna cin bulus, wannan ta sanya hantar ma’aikata da yawa ta kada domin ba kowane ke son bincike ba, a cewar wani dan siyasa ko danka ne akace zai yi maka bincike dole hankalinka ya tashi ballantana hukuma, amma ta wannan bangaren kam munyabawa mai girma gwamna domin bai kamata a kyale wasu haka kurum su rika karbar abin da ba hakkinsu ba.

Bayan haka kuma, gwamnan ya kirkiro da sabuwar jami’a a kano wadda aka sanyawa sunan North West University (jami’ar Arewa maso Yamma) hakika wannan ma wani muhimmin ci gaba ne da gwamnan ya kawo jihar kano kasan cewa kididdiga ta nuna cewa akalla akwai yara kusan Miliyan daya da suke makarantun sakandare daban-daban a fadin jihar kano, duk wanda ya kalli wannan alkaluma kuma yaga abinda gwamna ya yi dole ya yaba masa ta wannan gefen, dama wasu ayyuka da aka bijiro da su wanda sun cancanci a yaba akansu.

Amma a irin yadda gwamnan yake bita da kulli akan tsohon gwamna Sardauna wannan ya nuna kamar da gaske ne yazo ne domin ramuwar gayya. Domin sau da yawa akanji gwamnan na magana akan sabon gidan da gwamnati ta ginawa Sardaunan, dama mayarda hannun agogo baya akan wasu muhimman ayyuka da gwamnatin sardauna ta bari, musamman kasurgumin aikin nan na samar da babbar cibiyar harkar sadarwa da babu irinta a kasarnan wadda ake kira Kano ICT Park, bayan kashe dubban kudade akan wannan aiki amma da sabon gwamna ya zo ya yi buris da wannan aiki.

Hakama aikin da mai girma Sardauna ya kirkiro na ADAIDAITA SAHU wanda mai martaba sarkin kano ne jagoran wannan shiri, shi ma anyi burus dashi, hakan bazai bada mamaki ba domin Hausawa sunce barewa bazatayi gudu ba danta ya yi rarrafe, daman PDP ba kishin ‘yan Najeriya suke ba na kawar da matsala sai dai kawo sabuwar matsala, kaga sai muce anan albasa tayi halin ruwa, dama manufarsu ce wannan.

Bayan haka kuma, akwanakin baya aka kaiwa ofishin shiyya na kamfanin Media Trust da ke kano hari inda ake zargin daya daga cikin jami’an gwamnatin kwankwason da hannu cikin wannan aika-aika, kamar yadda itama gwamnatin tarayya ta PDP taje gidan tsohon Ministan Abuja Mallam Nasiru el-Rufai tayi masa aika-aika saboda ya shiga zanga-zangar nuna adawa da cire tallafin manfetur da gwamnatin tayi, duk wannan na kara nuna mana cewa lallaai albasa tayi halin ruwa idan dan PDP na kasa ya muzgunawa jama’a, domin a can saman ma haka abin yake.

Sannan ga maganar tashin bama-bamai a kano. Rahotannin sun tabbatar da cewa ‘yan kungiyar Boko Haram sune suka kai wadan nan muna nan hare-hare inda sukayi ikirarin kai wannan harin, a cewarsu har wasika sun aikewa da gwamnatin amma batayi komai akai ba. Kuma anan ne zamu zargi shi mai girma gwamna da sakaci babba ta fuskar tsaro domin tunda wannan kungiya suka bayarda wannan sanarwa babu wasu alamu da suka nuna andauki mataki na kare al’umma daga wannan barazana. Hakika dole gwamna ya dauki al’hakin sakaci da ya yi tabbas da andauki mataki da abin yazo da sauki, zakayi mamaki ace ajihar kano an daddasa bama-bamai har kusan guda hamsin a cikin birni kuma duk sun tarwatse amma a kasa gano lokacin da ake dasa wadan nan bama-bamai wannan abin akwai daure kai kwarai da gaske, muna fatar Allah ya kare aukuwar hakan anan gaba.

Sannan bayan wannan al’amari ankawo sojoji da ‘yan sanda masu yawan gaske da suke tsanantawa al’umma akan hanyoyin da aka sanya rodubulo, jama’a na gaggawar komawa gida domin gudun kada su karya dokar da aka sanya, amma ko ya ya mutum ya taka wannan doka sai ya sha wulakanci mai yawan gaske, wanda wannan dole gwamnati ta takawa abin birki. Allah ya taimaki jihar kano ya bamu lafiya da zaman lafiya, kuma muna addu’ar Allah ya shiryi shugabanninmu ya basu ikon cika mana alkawuran da suka dauka mana, ya kade mana fitina da tashin hankali.

Yasir Ramadan Gwale

yasirramadangwale@hotmail.com

http://yasirramadangwale.blogspot.com

No comments:

Post a Comment