Saturday, February 18, 2012

Sani Hashim Hotoro: Matsalar ANPP a Kano

Yanzu dai sanin kowa ne cewa ta faru ta kare dangane da dukkan wasu abubuwa da suka shafi babban zaben 2011, inda tuni ya zama tarihi kuma ya shiga kundin tarihin kasarnan, haka itama shekarar 2011 mukayi bankwana da ita sai dai wani jikon, haka kuma ‘yan siyasa da dama sun gwada kwarinsu a wannan zabe wasu ta kai musu inda suke ta murna da sowwa, wasu kuma sun rasa inda akayi aka haihu a ragaya jugun jugun. Hakika lokaci ya yi da yaka mata a zauna a kalli wasu dalilai ne ko matsalolin da suka janyowa jam’iyyar ANPP matsala a wannan zabe duk da muhimmiyar damar da ake da ita, ta cewa gwamna mai tafiya dan wannan jam’iyyar ne.

Zance na gaskiya akwai tarin matsaloli da suka janyowa wannan jam’iyya samun nakasu, kuma sannan ‘yan hamayya sunyi amfanii da propaganda domin kawo wa jam’iyyar matsala kuma sukayii sa’a suka cimma nufinsu. Misali fitacce masanin nan Gerhard Lensky a shekarar 1991 yace duk mutumin da yake son wani muhimmin abu yakanyi amfani da dukkan wasu hanyoyi da yake ganin idan ya bi su zai kai ga samun wannan abu, ta hanyar kama zukatan mutane da wasu abubuwa sabbi kuma masu sauki akan al’umma wadanda sukayi dai-dai da hankali da tunani. Haka kuma idan zamu iya tunawa shugaban kasar Amerika Barack Obama a lokacin da yake yakin neman zabe ya yi amfani da wasu kalamai da suka janyo masa karin farin jini da karbuwa a tsakanin Amurkawa, domin ya yi amfani da kalamar “Yes we can” ma’ana tabbas zamu iya. Kusan duk sadda ya fita yakin neman zabe zaiyi ta maimaita wannan kalma, haka har ta samu karbuwa a tsakanin Amurkawa kuma akaci sa’a wannan kalami ya kara masa karbuwa sosai.

Idan kuma muka dawo Kano, babban dan hamayya Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi amfani da wani take kamar yadda Obama ya yi wajen kama zukatan musamman matasa, wannan take shi ne kwankwasiyya amana, hakika kamar yadda Lensky ya fada dole mutum ya yi amfani da wani abu sabo kuma wanda zai dace da hankali da tunanin mutane domin kama zukatansu a lokacin da yake neman wani abu muhimmi. Idan muka dauki dan takarar gwamnan na PDP a jihar kwara Abdulfattah Ahmed shima ya yi amfani da wani take mai suna Legasy continues shima wannan ya yi tasiri kwarai da gaske wajen samun karbuwarsa. Inason a yimin kyakkyawar fahimta ba ina nufin dantakararmu baiyi amfani da irin wannan salo ba, a’a ko kadan bana nufin haka hasalima Mallam Salihu Sagir Takai ya yi amfani da wani salo na babu makami sai addu’a wanda a karshen lokaci aka zo da wannan take, wanda a hakikanin gaskiya taken da wahala ya sami karbuwa idan anbi bayanan manazarta sanin dabi’a da tunanin dan Adam, domin yadda Ibn Khaldun ya fada acikin littafinsa mai suna ‘mukaddima’ baka amfani da sunan wani adu da kasan hadari ne ga al’umma domin samin amincewarsu, komai kyan abinda zaka fada kuwa, tana iya yiwuwa Ibn Khaldun shima ya yi kuskure a wannan ra’ayin nasa, domin ba fadar Allah bace.

Haka kuma, muna kallon yadda aka rinka yakar Mallam salihu ta kowanne bangare. Domin daga cikin irin propagandar da akayi amfani da ita kuma tayi tasiri a zukatan mutane ita ce cewa jama’ar kano basa son Takai, sukayi ta kururuta wannan magana wanda duk munsan karya ne, daga karshe har mutane suka fara gamsuwa cewa Takanannanfa ba’a sonsa ya kamata mai girma gwamna ya sauyashi daga cikin wadan da suka rudu kuwa harda da yawa daga cikin ‘yan ANPP, kaga wannan anyi amfani da wani abu da ba gaskiya bane domin a kullum shi abokin adawarka neman wata hanya yake da zai sare maka guiwa a wajen jama’a, don mai-makon kayi tallar manufofinka sai ya canza maka akala inda zaka koma kare kanka da nuna cewa abinda yake fada akanka ba gaskiya bane, shi kuma a gefe guda yana ci-gaba da yada nasa manufofin.

Sannan kuma, aka sami wani bangare acikin jam’iyyar ANPP wadan da ake kira ‘yan tabare wanda abinda da sukeyi kamar kara gishiri ne a cikin garin ‘yan adawa, amma uwar jam’iyya tana kallo batayiwa wannan tufkar hanci ba duk da ‘yan boko da dumbin masana da muke da su a cikin wannan tafiya, inda suma sukaci nasarar kama zukatan al’umma da wadan nan kalamai. Baya ga haka akazo ana cewa Mallam Salihu mai hannun jarirai ne haka shima akayi amfani da dama aka dauke hankalinmu daga bayyana hakikanin manufarmu ga al’umma zuwa nuna cewa abin ba haka bane.

Sannan idan muka kalli wani salo da PDP suka yi amfani da shi wajen kama zukatan matasa a wannan zabe shi ne, duk kankantar masoyin PDP da kwankwasiyya basa wasa da shi, domin nasan wani da yana da ra’ayin wannan tafiya ta su, duk da baima gama fahimtar kansa ba, amma suka daukeshi da muhimmanci, haka zakaga suna gayyatarsa zuwa dukkan irin tarukan da suke yi, anan sai na lura da cewa gaskiya su basa wasa da magoyin bayansu komai kankantarsa, domin shi wannan yaro ya shirya wani taro na motsa ‘yan jam’iyya amma idan kaga manyan mutanen da suka halarci wannan taro abin zai baka mamaki, kaga ko babu komai wannan kara kaimi ne ga matasa masu goyon bayansu, kamar yadda Max Weber ya ce duk dan adam yana son ka bashi kima da girmansa, wannan zata sanya kaci nasara akansa.

Idan kuma muka kalli bangaren ANPP ta wannan janibi, zance na gaskiya basuyi komai akansa ba, don basu cika baiwa kana nan magoya baya muhimmanci ba, wadan da kuma sune abokan tafiya sune sarakan yaki, domin wasu manyan mutanan idan da zasu zo taro ko bazasu ce komai ba wani karin karfin guiwa ne ga magoya baya. Wallahi Allah ya albarkaci wannan tafiya da mutane masu akida ta gaskiya wadan da ba wani abu suke son a basu ba illa kawai kwarin guiwa da karfafasu, domin nasan matasan da suka taimakawa wannan tafiya da kudinsu da lokacinsu da tunaninsu, ba su da niyyar su sami wani abu idan ankai ga gaci, amma jam’iyya batayi wani abu na kuzo mu ganiba wajen binkitosu tare da karfafamusu guiwa.

Manyan shugabannin wannan jam’iyya suna maida hankali ne ga manyan ‘yan jam’iyya. Mutanan da wallahi wasu ko zaben basa fita suyi, suna gida a kwance suna tsegumi, kuma yana daga cikin nasarar ‘yan PDP da suka kama zukatan matasa da mata shi ne duk abin da aka basu domin su rabawa al’umma sukanyi iyakar kokarinsu wajen hakan, amma wallahi nasan ‘yan ANPP da dama wadan da za’a basu wani abu su raba amman zasu jibge agida suda iyalansu, ina fatar za’a yimin afuwa akan wannan magana, domin wallahi kishin Mallam Salihu Sagir Takai ya sanyani rubuta wannan koke, amma dai ina ganin lokaci ya yi da zamu fadi gaskiyar al’amura domin samin mafita a lokaci na nan gaba.

Wata rana na tattauna da wani abokina akan wannan tafiya ta Mallam Salihu, ya shaidamin cewa matsalar shugabannin jam’iyyar ANPP shi ne suna da raina magoya baya, nace masa hakika ka fadi gaskiya domin a irin yadda nake kallon shugabannin jam’iyya na jiha da kananan hukumomi basu dauki magoyin baya a bakin komai ba, domin zakaga wannan unguwar akwai daya daga cikin shugabannin jam’iyya ko dai a mataki na jiha ko na karamar hukuma kuma ga masoya na hakika sai kaga babu ruwansa da su; wanda irin wadan nan mutane ‘yan PDP suke saurin ribata a karon farko.

Kamar yadda wannan sakamakon zabe ya nuna idan har kotu ta tabbatar da shi cewa ba mune mukayi nasara ba wanda bana fatan hakan, to ya nuna cewa lallai Mallam Salihu Sagir Takai da Dr. Bashir Shehu Galadanci suna da dumbin magoya baya domin samun adadi irin wannan mai yawa da yakai sama da Miliyan daya to kuwa bai kamata a yi sakaci har ya zogaye ba, ya kamata a tsaya a kalli hanyoyin da suke na hakika wadan da za’a bi wajen tufke barakar da ake da ita da kuma dinke dukkan wata matsala da ake da ita. Hakika akwai ‘yan jam’iyyar da sunyi kokari wajen ganin wannan tafiya ta sami nasara, bai kamata a kyale su ba, ya kamata a cigaba da karfafa musu guiwa tare da tabbatar da su, anan nima nake son yin amfani da wannan damar wajen yin jinjina ga Hon. Dr. Musa Iliyasu Kwankwaso domin hakika yana daga cikin mutanan da suka bayar da gudunmawa babu dare babu rana wajen samun nasarar wannan tafiya, haka shima Alhajin Baba (taimako) ya cancanci yabo domin yayi iyakar yinsa wajen samun nasarar wannan tafiya da sauran duk wadan da suka baiwa wannan tafiya gudunmawa a zahiri ko a badini.

Sannan bazan mance da mutane irina wadan da muka baiwa wannan tafiya dukkan irin gudunmawar da ta halatta a garemu ba tare da fatan samun wani abu ba a matsayin return, ina jinjina ta musamman ga kananan kungiyoyi na tafiyar Mallam Salihu, Hakika ayyukanmu da addu’armu bazasu tafi a banza ba insha Allah.

Daga kashe, ina mika wannan koke nawa ga mai girma shugaban jam’iyyar ANPP Alh. Sani Hashim Hotoro da cewa lallai ya kamata a tsaya a kalli irin matsalolin da muka fuskanta a wannan tafiyar da kuma hanyoyin da za’a bi wajen kawo gyara, kuma muna tabbatar muku cewa wallahi muna nan tare da wannan tafiya ta Mallam Salihu Sagir Takai da Dr. Bashir Shehu Galadanci. Zan rufe da baitin wata waka da wani mawaki ya yiwa wannan tafiya cewa “takai da galadanci ayari na alkhairi ya zowa kanawa” Allah ya tabbatar mana da wannan ayari da kuma alkhairin da ke cikinsa. Muna tawassali da sunayen Allah tsarkaka, madaukaka, Allah ya karbi addu’o’inmu ya tabbatar mana da alheri ko a yanzu ko a nan gaba.

Yasir Ramadan Gwale

yasirramadangwale@gmail.com

http://yasirramadangwale.blogspot.com

No comments:

Post a Comment