Friday, February 10, 2012

Mallam Nuhu Ribadu: Juma’ar da za ta yi kyau . . .!

Mallan Nuhu Ribadu


A wata magana mai cike da armashi ta Bahaushe yana cewa, sai an shiga cikin rijiya sannan ake iya yashe ta, babu wanda zai iya yashe rijiya daga waje face ya shiga cikin ta, idan ta kama ma har ya bata kayansa. . . Mallam Nuhu Ribadu kamar yadda kowa ya sani shi ne dan takarar Shugaban kasa a karkashin jam’iyyar ACN a zaben 2011 da ya gabata. Kafin zamansa dan siyasa Ribadu tsohon ma’aikacin hukumar ‘yan sanda ta kasa ne, wato ya kai har mukamin mataimakin kwamishinan ‘yan sanda, inda bayanai suka nuna har tsallaken mukami akayi masa daga mataimakin kwamishina zuwa mataimakin sifeto janar na rundunar ‘yansada na kasa saboda kwazonsa da kwarewa wajen iya aikinsa.

Sunan Mallam Nuhu Ribadu ya fara bayyana ne a lokacin da ya jagoranci hukumar yaki da yiwa tattalin arzikinsa zagon kasa da kuma yakar cin-hanci da rashawa, wadda akafi sani da EFCC, hakika ya nuna kwazo sosai lokacin da ya shugabanci wannan hukuma, domin ya kama tare da gurfanar da mutanan da ake ganin baza su iya tabuwa ba a kasarnan, bisa zarginsu da yin almundahana da dukiyar kasa. Misali bayan da sashi na 308 na kundin tsarin mulkin kasar nan ya baiwa masu rike da mukamin shugaban kasa da mataimakinsa da gwamnoni kariya daga gurfana gaban kowane irin kwamitin bincike, Ribadun yace kusan daukacin gwamnonin kasarnan barayi ne, da kuma shugabannin kananan hukumomi domin sunyi rubdaciki da dukiyar al’umma tunda yake bashida ikon kamasu ya gurfanar da su, shakka babu wannan ba karamin aiki ya yi ba, ko iya nan ya tsaya.

Sai dai ya kama tare da garkame wasu daga cikin gwamnonin da kuma tonawa wasu asiri, haka kuma da yawa daga cikin manyan attajiran kasarnan da suke ci-da gumin talakawa ya tona musu asiri, kuma da yawa sun shiga taitayinsu don ya diga ayar tambaya ga wasu daga cikin hamshakan attajiran nan irinsu Femi Otedola da Mike Adenuga da Muhammad Babangida da ya mallaki hannun jari mai yawa a wasu kamfanoni a kasar Ingila wanda mujallar Times Magazine ta wallafa.

Bayaga damke tsohon gwamnan jihar Bayelsa DSP Aliemieghsigha, ya kuma kama takwaransa na Jihar Delta Mista Jame Ibori wanda ake ganin babu wanda ya tallafawa takarar marigayi YarAdua da kudi irinsa, Ribadun karkashin hukumarsa ya zargesu da zambar kudi kusan dubban miliyoyin daloli, rahotanni sun nuwa cewa Mista Ibori ya yi kokarin baiwa Ribadu toshiyar baki ta wasu makudan kudi amma Ribadun yaki karba. Sannan kuma ya fallasa irin adadin kudaden da gwamnoni sukayi rubdaciki da su a yayin da suke kan mukamansu, misali inda ya bayyana tsohon gwamnan Jihar Jigawa Ibrahim Saminu Turaki ya yi almundahana da kusan Naira Biliyan 36, da sauran gwamnoni da daman gaske ya yinda wasu kuma suka arce suka bar kasarnan wanda suka hada da tsohon gwamnan Jihar Edo Mista Locky Igbinideon da Adamu Mu’azu na jihar Bauchi da sauransu da dama a wancan lokacin.

Haka kuma, aikin da hukumar EFCC da Mallam Nuhu Ribadun ya jagoranta ya sanya sunan Najeriya da yayi kaurin suna wajen cin hanci da rashawa ya dan samu sararawa sakamakon hukumar dake kididdige adadin kasashen da sukafi cin hanci da rashawa ta duniya suka sassauto da sunan Najeriya daga matakin koli zuwa na kasa-kasa. Hakika Mallam Nuhu Ribadu ya yi kokari wajen yakar cin hanci da rashawa a lokacin da ya rike wannan hukuma, sai dai da dama sunga laifinsa akan cewa kamar ana amfani da shi ne wajen muzgunawa masu adawa da gwamnatin Obasanjo ta wancan lokacin.

Amma dai ko me jama’a zasu ce akan wannan aiki Mallam Ribadu ya yi rawar gani, domin ita barna ko da kashi daya cikin dari aka rage ta anyi aiki, sanin kowane a yadda sunan Najeriya ya baci da cin hanci da rashawa babu yadda za’a iya yakarsa cikin lokaci kankani, hakika dole a yaba masa. Idan ba’a mantaba har ‘yar shugaban kasa Obasanjo a wannan lokacin Ribadun ya zarga da cin hanci da rashawa, wanda, idan da babu alamun gaskiya a tattare da shi da dawahala ya yi hakan.

Wannan ce ma ta sanya majalisar Dinkin Duniya ta zabi Ribadun a matsayin wanda zai jagoranci wata tawaga da zata tafi ya zuwa Afghanistan domin aikin sanya ido da kuma bankado cin hanci da rashawa a wannan kasar, hakika idan da bashida kwazon aiki ko kuma yanada alamu na rashin gaskiya da wahala ya samu wannan muhimmin aikin aikin.

A lokacin da gwamnati ta bayar da sanarwar sunasa a matsayin mutumin da aka nada wanda zai jagoranci mutane 21 domin sanya ido da kuma bayarda bayanai akan rarar kudin mai, jama’a da dama sukayi ta tofa albarkacin bakainsu akan wannan batu. A cewar Mallam Nuhu Ribadu ya samu dimbin sakonnin waya da na imel da kira akan wannan sabon mukami da gwamnati ta bashi, wasu su karfafa masa guiwa ya karba wasu kuma su ce kada ya karba, har dai ya yanke hukuncin zai karbi wannan muhimmin aikin bayan da ya yi shawara da makusantansa da kuma mutanan da yake ganin zasu bashi shawar ta gari, sannan ya kira wannan aikin da sunan wata sabuwar dama ta bankado cin-hanci da rashawa a harkar manfetur da aka dade ana zargin hukumar NNPC da aikatawa.

Bayan da aka bayyana sunansa a matsayin sabon shugaban wannan hukama ta Petropleum Revenue Special Task Force, jama’a da dama suka shiga maida martani akan wannan batu, wasu na cewa daman aiki ya yiwa PDP a sakamakon fitowarsa takarar Shugaban kasa domin ya raba kan kuri’ar Arewa ko kuma ya kawowa Buhari cikas, dama wasu zarge-zarge da dama wadan da basu da tushe. Hakika Mallam Nuhu Ribadu ya cancanci ya karbi irin wannan muhimmin aiki domin tarihinsa ya nuna zai iya, kamar yadda yace kusan duk rayuwarsa ya taso yana hidimane ga kasarsa kamar yadda ya buga misali yace ya gada ne daga mahaifinsa; domin mahaifinsa daga Danmajaisar tarayya daga Legas a jamhuriya ta farko ya dawo Yola domin rike wani dan karamin kwamitin da zai tallafawa rayuwar al’umma.

Da yawanmu muna fatar samun gyaruwar al’amuran kasarnan, amma kuma da yawan mutanan kwarai sukan kame hannayensu daga yunkurin kawo gyara. Idan har mutanan kirki zasu nade hannu suce su baza su shiga gwamnati a kawo gyara tare da su ba, ko shakka babu za’a jima gyara bai zoba domin babu yadda gyara yake zuwa lokaci guda. Misali sanin kowane da Abacha da Babangida suka hada baki aka kifar da gwamnatin Buhari a 1981 amma wannan bata hana Buharin ya karbi aikin da gwamnatin Abacha ta bashi na hukumar tara kudin rarar man fetur ta PTF ba wanda kowa yasan wannan hukuma tayi aiki na azo a gani, abin tambaya da Buhari ya kame hannunsa yaki karbar wannan aiki za’a samu gyara ta wannan bangare? Shakka babu amsar itace a’a, don haka ba laifi bane idan har Nuhu Ribadu da ya yi takara tare da Jonathan kuma ya karbi aiki a gwamnatinsa domin tallafawa rayuwar ‘yan Najeriya da kuma hidima ga kasarsa ta haihuwa.

Idan zamu iya tunawa a lokacin da akayi zabe tsakanin Tsohon Shugaban kasar Amerika George W. Bush daga jam’iyya Refublican da kuma John F. Kerry daga jam’iyyar Democrat, a shekarar 2004, da John Kerry bai sami nasara ba ya yi aiki a kwamitoci da dama a gwamnatin ta Bush bayan kasancewarsa dan majalisar dattijai, haka shima John McCain ya yi ayyuka a kwamitoci daban-daban a wannan gwamnatin ta Barack Obama wannan ya nuna cewa lallai idan ana batu na ginin kasa da kuma ci gabanta babu siyasa a ciki kowa ajiye jam’iyya yake yi a hadu a gina kasa tare, a gudu tare a kuma tsira tare.

Sabida haka ina ganin kuskure ne mutane su zargi Nuhu Ribadu akan wannan aiki da aka bashi, adaidai lokacin da kasarnan ta ke da bukatar mutane masu gaskiya wajen alkinta dukiyar al’umma, ko babu komai jama’a sun shaida irin aikin da yayi a lokacin da ya rike EFCC abinda zai tabbatar da hakan mu kalli wadan da suka biyo bayansa a wannan hukuma, kowa cewa yake gwara Ribadun akan musamman ita Farida waziri da ta biyo bayansa da kuma shi Mallam Ibrahim Lamode duk da cewa sabone bai dade ba.

Don haka, muna taya dan uwanmu Mallam Nuhu Ribadu murna tare da fatan alheri a wannan sabon aiki da ya samu mai cike da kalubale. Muna fatar zai yi aiki fiye da wanda ya yi a EFCC wanda duniya ta yaba masa kwarai da gaske, kuma muna masa addu’ar Allah ya kareshi daga dukkan wani sharri ya kuma bashi kwarin guiwar yin aiki bisa gaskiya da adalci. Allah ya taimaki kasarmu Najeriya ya bamu lafiya da zaman lafiya, ya kuma shiryi shugabanninmu ya sanya musu tsoronsa da kuma basu ikon sauke nauyin da yake kansu na al’umma.

Yasir Ramadan Gwale

yasirramadangwale@hotmail.com

http://yasirramadangwale.blogspot.com

No comments:

Post a Comment