Friday, August 14, 2015

KATSINA: Gwamnan Canji Masari Ya Fara Da Aika Aika


KATSINA: MASARIN CANJI YA FARA AIKA AIKA 

Jaridar Daily Trust ta ranar Juma'a 14 ga watan agusta ta ruwaito cewar sabon zababben Gwamnan Jihar Katsina Aminu Bello Masar ya amince da fitar da kudi Naira Biliyan Daya da Miliyan dari takwas dan yin Kwaskwarima ga Gidan Gwamnatin Jihar Katsina.

Gwamna Masari na wannan aiki ne a daidai lokacin da yake kalubalantar tsohon Gwamna Ibrahim Shehu Shema da yin almubazzaranci da dukiyar al'ummar jihar, a kuma lokacin da ake cewa ana tsuke bakin aljihun Gwamnati dan rage kashe kudin al'umma ba gaira babu dalili.

Ashe dai na Gwamnan Kano Ganduje Nafila ne, a lokacin da muka kalubalance shi kan kashe Naira Miliyan 180 dan yiwa sabuwar turakar mataimakinsa kwaskwarima. Allah ya kyauta.

Yasir Ramadan Gwale 
14-08-2015

No comments:

Post a Comment