Tuesday, August 11, 2015

KANO: Gwamna Ganduje Ya kaddamar Da Mummunan Yaki Akan Kwankwaso


KANO: GANDUJE YA KADDAMAR DA MUMMUNAN YAKI KAN KWANKWASO

Jaridar Vanguard ta ranar asabar 9 ga watan Agusta, ta ruwaito cewar, wani mummunan yakin cacar baki ya kaure tsakanin gwamnan Kano magabaci Sanata  Dr. Rabi'u Musa Kwankwaso​ da kuma Gwamna mai ci Dr. Abdullahi Umar Ganduje OFR​. Wannan mummunar musayar yawu dai ta zo ne a lokacin da kungiyar daliban Arewacin Najeriya da ke karatu a kasar Masar suka kaiwa Gwamna Gandujen ziyara a ofishinsa a makon da ya wuce.

Gwamna Ganduje yace, tsohon mai gidansa Sanata Kwankwaso ya kai yara 'yan asalin jihar Kano Karatu kasashen waje daban daban, amma ya yi tafiyar ruwa da kudinsu  kimanin Naira Biliyan uku. Gwamna yace halin da daliban suke ciki na rashin biya musu kudi ba laifinsa bane, laifin Kwankwaso ne.

 Wannan batu dai a cewar Vanguard ya janyo wani kazamin Martani daga bangaren tsohon Gwamna Dr. Rabiu Musa Kwankwaso, wanda tunda ya tafi Abuja bai sake zuwa Kano ba. Wasu bayanai sun nuna cewar Gwamna gwanduje ya sha alwashin fede biri har wutsiyarsa game da wannan batu na kudin daliban da Kwankwaso ya tura waje Karatu.

Yasir Ramadan Gwale
09-08-2015

No comments:

Post a Comment