Tuesday, July 14, 2015

Yakar Boko Haram


YAKAR BOKO HARAM
Babbar matsalar da ta addabi mutanan Nigeria ita ce wannan fitinar ta Boko Haram, har ma da kasashe ma'kwabtan Najeriya. Shi mai aikata laifi musamman irin na ta'addani irin na Boko Haram dabaru gareshi iri iri, a lokacin da jami'an tsaro ko Gwamnati ke k'ara shirin tunkarar wannan Ya'ki gadan gadan, suma a nasu bangaren 'yan Boko Haram ba wai kawai zaune suke suna jiran mutuwa ba.
Kamar yadda bayanai suka nuna cewar itama Boko Haram a yanzu kara shiri suke, domin had'akarsu da k'ungiyar ISIS babbar barazana ce ba ga Nigeria kad'ai ba har da ma'kwabtanmu. Alhamdulillah a yau abinda aka jima ana jira ya tabbata, na sauya jama'an tsaron da PMB ya gada daga Gwamnatin da ta shud'e. Wad'annan sabbin nad'e nad'e da akai an ce galibinsu sun fito daga yankin Arewa Maso Gabas, wanda fatanmu shi ne Allah ya basu ikon murkushe Boko Haram da karfin Allah.
Ba shakka, idan akwai abinda ya kamata mu dage da adduah akansa bai wuce samun zaman lafiya a Najeriya ba. Muna fatan Allah ya baiwa wad'annan jagorori Nasarar dirkake Boko Haram, Allah ka azurtamu da samun zaman lafiya mai d'orewa a kasarmu. Ya Allah Kada ka baiwa 'yan ta'adda nasara komai kaskantar ta. Allah ka baiwa sojojin Najeriya nasara akan wannan Yaki.
Yasir Ramadan Gwale
13-07-2015

No comments:

Post a Comment