Thursday, July 16, 2015

Labari MARAR Dadi Daga Gombe


LABARI MARAR DADI DAGA GOMBE 

A daidai lokacin da al'umma ke fara shirin Sallah karama a gobe a duk fadin duniya, muka samu mummunan labarin harin Bom da aka kai tsakiyar kasuwa a Jihar Gombe! Wannan babban abin bakinciki ne da takaici ainun, abin akwai Kada zukata a yayin da al'umma ke d'oki da ganin anyi Sallah lafiya, wasu miyagun azzalumai mabiya Tafarkin shedan suke ta kokarin kawo karshen rayuwar mutanan da basu ji ba basu gani ba ta irin wannan mummunar hanya. Allah ya jikan wadan da suka rasu, muna mika ja je da ta'aziyar mu ga Gwamnatin Jihar Gombe da al'Umar jihar baki daya. Allah ka kawo mana karshen wannan tashin hankali da ya addabemu.  

Yasir Ramadan Gwale 
16-07-2015

No comments:

Post a Comment