Saturday, July 11, 2015

SA'UDIYYA : Sarki Salman Bin Abdulaziz Ya Jagoranci kaddamar da aikin fadada Masallacin Haramin Makkah Da Zai Kunshi Masallata Miliyan Biyu Ba Dubu Maitan


SARKI SALMAN YA K'ADDAMAR DA AIKIN FADADA HARAMIN MAKKAH DA ZAI KUNSHI  MASALLATA MILIYAN BIYU BA DUBU MAITAN 

Ranar Asabar 12 ga watan Yuli bayan da ya sha ruwa a Makkah, Sarki Salman Bin Abdulaziz ya jagoranci kaddamar da aikin fadada Masallacin Haramin Makkah da zai kunshi Masallata Miliyan biyu ba Maitan. Sarkin ya bayyana cewar wannan aikin shi ne zai bayar da damar gagarumin aikin fadada Masallacin da zai kunshi Masallatai Miliyan biyar nan da shekaru goma masu zuwa.

Da yake jawabi a wajen taron Babban Limamin Haram Sheikh Abdurahman as-Sudais (Imam of Masjid alHaraam, Makkah)​ ya bayyana cewa wannan shi ne katafaren aikin fada da Masallacin ka'aba da ba'a taba yin sa ba. Kuma shi ne, na uku a cikin manyan ayyukan fada da Masallacin tun bayan wanda  Sarki Fahad da Abdullah suka yi. Sheikh Sudais ya yabawa Sarki Salman akan wannan aiki tare da yi masa adduar fatan alheri akan kulawar da yake baiwa Masjid al-Haram​, sannan ya kara da cewa kamar yadda kasar Saudi Arabia​ ke kan tsarin Sunnah, ya sha alwashin ci gaba da tafiyar da Masallacin a bisa tsarin Sunnah.


A nasa jawabin Sarkin Kuwait Sheikh Sabah Ahmad Al-Sabah ya gode wa Sarki Salman da kuma Masarautar Sauin a bisa irin wannan kulawa da suke baiwa Haramain dake Makkah da Madina. Sarakunan Bahrain da Dubai​ duk sun aiko da sakon fatan alheri ga Sarki Salman akan wannan katafaren aiki.

YASIR RAMADAN GWALE​
12-07-2015

No comments:

Post a Comment